Kotun daukaka kara ta tabbatar da Yahaya Bello a matsayin gwamnan Kogi

Kotun daukaka kara ta tabbatar da Yahaya Bello a matsayin gwamnan Kogi

Kotun daukaka karar zaben gwamnan jihar Kogi da ke zamanta a Abuja, ta yi fatali da kararraki hudu da ke kalubalantar zaben Gwamna Yahaya Bello wanda ya mai do shi kujerar mulki a wa'adi na biyu.

Kotun a yayin zamanta da ta gudanar a ranar Asabar cikin birnin Abuja, ya tabbatar da nasarar Yahaya Bello a matsayin zababben gwamnanjihar Kogi.

Jam'iyyu hudu da suka kalubalanci sakamakon zaben ta hanyar shigar da korafinsu a gaban kuliya sun hadar da PDP (Peoples Democratic Party), APP (Actions People’s Party); SDP (Social Democratic Party) da kuma DPP (Democratic People’s Party).

Yayin zartar da hukunci daban-daban Alkalan kotun biyar karkashin Mai Shari’a Adamu Jauro, sun yi watsi da kararrakin hudu saboda rashin dalilai masu tushe.

Gwamnan jihar Kogi; Yahaya Bello
Gwamnan jihar Kogi; Yahaya Bello
Asali: UGC

Jaridar Premium Times ta ruwaito cewa, an yi watsi da karar da dan takarar jam’iyyar PDP a zaben, Musa Wada ya shigar, bayan ya gaza tabbatar da zarginsa na cewa an yi magudi a zaben.

Da yake zartar da hukunci, Mai Shari'a Muhammad Shu'aibu, ya yi fatali da korafin da jam'iyyar APP da DPP suka shigar na zargin hukumar zabe ta kasa mai zaman kanta INEC ta cire sunayensu a zaben.

Kotun daukaka karar ta kuma yi watsi da karar neman soke zaben da 'yar takarar jam'iyyar SDP Natasha Akpoti ta shigar, yayin da ta gaza bayar da kwarararn hujjoji na zargin saba ka'idoji.

KARANTA KUMA: Dalilin da ya sa Najeriya ba za ta daina karbo bashi ba - Ministar Kudi

A karshe kotun ta nemi dan takarar jam'iyyar PDP; Musa Wada, da ya biya naira dubu 100 ga kowane daya daga cikin wadanda ya yi korafin a kansu da suka hadar da; Gwamna Bello, jam'iyyar APC da kuma hukumar INEC.

Ana iya tuna cewa, a zaben gwamnan jihar Kogi da aka gudanar a watan Nuwamba na shekarar 2019, Mista Bello ya lashe kuri'u 406,222 inda ya tika abokin karawarsa da kasa, na jam'iyyar PDP Mista Wada, da ya tashi da kuri'u 189,704.

'Yar takarar jam'iyyar SPD, Misis Akpoti, ta zo ta uku yayin da aka fidda sakamakon zaben inda ta samu kuri'u 9,482.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel