Sunaye: Buhari ya sake aikawa majalisa sabbin sunayen mutane 42 a matsayin jakadu

Sunaye: Buhari ya sake aikawa majalisa sabbin sunayen mutane 42 a matsayin jakadu

Shugaban kasa, Muhammadu Buhari, ya nemi amincewar majalisar dattijai domin ta tabbatar da sunayen mutane 42 da ya ke son kara nadawa a matsayin jakadun Najeriya a kasashen ketare.

Daya daga cikin mutanen da shugaba Buhari ya aika sunansu zai kasance jakada mai cikakken iko a yayin da sauran mutanen 41 za su kasance jakadu na wucin gadi.

Daga cikin jakadun da za a nada akwai tsohon minista daga jihar Legas; Ademola Seriki, Debo Adesina daga jihar Oyo, Dare Sunday-Awoniyi daga jihar Kogi, da sauransu.

Sunaye: Buhari ya sake aikawa majalisa sabbin sunayen mutane 42 a matsayin jakadu
Buhari da wasu hadiman gwamnatinsa
Asali: Facebook

Ga cikakken jerin sunaye da jihohin mutanen da shugaba Buhari ya aikawa majalisar a ranar Laraba, 01 ga watan Yuli;

1. Umar Sulieman, Adamawa

2. L. S Mandama, Adamawa

3. Oboro Akpabio, Akwa Ibom

4. Elejah Onyeagba, Anambra

5. Abubakar Siyi, Bauchi

6. Philip Ikurusi, Bayelsa

7. Tarzoor Terhemen, Benue

8. Paul Adikwu, Benue

9. Al-Bishir Al-Hussain, Borno

10. Bwala Bukar, Borno

11. Monique Ekpong, Cross River

12. Oma Djebah, Delta

13. Ominyi Eze, Ebonyi

14. Yamah Musa, Edo

15. C. O Ugwu, Enugu

16. Hajara Salim, Gombe

17. Obiezu Chinyerem, Imo

18. Ali Magashi, Jigawa

19. M. A Markarfi, Kaduna

20. Hamisu Takalmawa, Kano

21. Jazuli Gadalanci, Kano

22. Amina Kurawa, Kano

23. Yahaya Lawal, Katsina

24. Dare Sunday Awoniyi, Kogi

25. Ibrahim Laaro, Kwara

26. Abioye Bello, Kwara

27. Zara Umar, Kwara

28. Ademola Seriki, Lagos

29.Henry Omaku, Nasarawa

30. Sarafa Isola, Ogun

31.Nimi Akinkube, Ondo

32. Adejaba Bello, Osun

33. Adeshina Alege, Oyo

34. Debo Adeshina, Oyo

35. Folakemi Akinyele, Oyo

36. Shehu Yibaikwal, Plateau

37. Maureen Tamuno, Rivers

38. Faruk Yabo, Sokoto

39.Adamu Hassan, Taraba

40. Yusuf Mohammed, Yobe

41. Abubakar Moriki, Zamfara

A cikin wata ta daban, shugaba Buhari ya bukaci majalisar dattijai ta amince da nadin sabbin kwamishinoni uku a hukumar daidaito a rabon mukami da daukan aiyuka a gwamnatin tarayya (FCC).

DUBA WANNAN: Buhari ya nada sabon shugaban cibiyar kasuwanci ta NEPZA

Kazalika, a wata wasikar mai zaman kanta, shugaba Buhari ya bukaci majalisar ta amince da nadin kwamshina guda daya da ya yi a hukumar kasafta kudaden rabanu da gwamnatin tarayya (RMAFC).

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel