'Ya'yan El-Rufai sun caccaki Atiku bayan dan sa ya yi wa El-Rufai habaici

'Ya'yan El-Rufai sun caccaki Atiku bayan dan sa ya yi wa El-Rufai habaici

'Ya'yan Gwamna Nasir El-Rufai, Bashir da Bello, sun caccaki tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, bayan daya daga cikin 'ya'yansa ya yi wa mahaifinsu habaici.

Dan Atiku Abubakar mai suna Mustapha, ya yi martani a inda El-Rufai ke shawartar iyaye da su koyar da 'ya'yansu girmama mata tun suna kanana.

A cewar gwamnan, hakan ne kadai zai iya dakile annobar fyade da ke tashe a kwanakin nan.

Babu kakkautawa Mustapha Atiku ya je yayi tsokaci a kasan wallafar inda yace "Abun mamaki".

Babu jimawa kuwa Bashir El-Rufai ya yi martani inda ya kira sunan Atiku tare da cewa "Irin wannan abun mamakin ne ke faruwa a duk lokacin da mahaifinsa ya yi magana a kan rashawa."

Ba tare da bata lokacin ba, Bello El-Rufai ya je ya yi nasa martanin mai zafi inda yace, "Bash, zancen ana yinsa ne a kan darajar mata ba luwadi ko rashawa ba.

"Kada ka damu da sabon angon, tsohon abokin naka ya yi tunanin a yanzu yana fadar shugaban kasa inda yake da daman kaiwa ga NNPC kai tsaye."

'Ya'yan El-Rufai sun caccaki Atiku bayan dan sa ya yi wa El-Rufai habaici
'Ya'yan El-Rufai sun caccaki Atiku bayan dan sa ya yi wa El-Rufai habaici. Hoto daga shafin Linda Ikeji
Asali: Twitter

'Ya'yan El-Rufai sun caccaki Atiku bayan dan sa ya yi wa El-Rufai habaici
'Ya'yan El-Rufai sun caccaki Atiku bayan dan sa ya yi wa El-Rufai habaici. Hoto daga shafin Linda Ikeji
Asali: Twitter

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng