An fasa kara farashin wutar lantarki a Najeriya

An fasa kara farashin wutar lantarki a Najeriya

Majalisar dattijai ta sanar da cewa ta samu nasarar shawo kan kamfanonin rarraba hasken wutar lantarki (DisCos) a kan yunkurinsu na kara kudin wutar da su ke bawa jama'a.

A cikin wani jawabi, Ola Awoniyi, kakakin shugaban majalisar dattijai, Ahmad Lawan, ya ce an cimma yarjejeniyar janye karin wutar yayin taron shugabancin majalisa da wakilan DisCos

Tun a cikin wtan janairu, hukumar kula da rarraba hasken wutar lantarki a Najeriya (NERC) ta sanar da cewa za a kara kudin wutar lantarki a fadin kasar nan daga ranar 1 ga watan Afrilu.

Amma sai sanarwa ta fito daga NERC a cikin watan Maris wacce ta umarci DisCos su dakatar da kara farashin wutar lantarki saboda bullar annobar korona.

An fasa kara farashin wutar lantarki a Najeriya
Ahmed Lawan
Asali: Facebook

Daga bisani, ministan wutar lantarki, Sale Mamman, ya ce sabon karin farashin wutar lantarkin zai fara aiki ne daga ranar 1 ga watan Yuli.

DUBA WANNAN: EFCC: Kotu ta yi barazanar janye belin tsohon Sanata Shehu Sani

Yayin zaman da aka yi tsakanin shugabancin majalisar dattijai da sauran ma su ruwa da tsaki a bangaren wutar lantarki, an lallami DisCos sun hakura da batun karin har sai zuwa farkon shekarar 2021 saboda annobar korona.

A wani labarin da Legit.ng ta wallafa, gwamnatin tarayya ta ce za a cigaba da rufe makarantun kananan yara da makarantun firamare da ke fadin kasar nan.

A sanarwar da ta fito kafin wannan, gwamnatin tarayya ta ce za a bude makarantu daga matakin firamare zuwa sakandire domin bawa daliban da ke shekarar karshe damar rubuta jarrabawa.

Sai dai, a cikin wata sanarwa da Dakta Sani Aliyu, jagoran kwamitin yaki da annobar korona a kasa, ya fitar a Abuja ya ce ba za a bude makarantun kananan yara da makarantun firamare ba.

"Ba za a bude makarantun kananan yara da makarantun firamare ba har sai sanarwa ta gaba," a cewarsa.

A baya Legit.ng ta wallafa cewa gwamnatin tarayya ta amince da bude makarantu a fadin kasar nan.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng