Annobar korona: Sanata Ndume ya bukaci FG ta rage albashin ma'aikata

Annobar korona: Sanata Ndume ya bukaci FG ta rage albashin ma'aikata

Ali Nudume, sanata mai wakiltar mazabar jihar Borno ta kudu, ya bukaci gwamnatin tarayya ta zabtare albashin ma'aikata.

Da ya ke magana a wani shirin gidan talabijin na 'Channels', Ndume ya ce bai kamata gwamnati ta ke biyan ma'aikata cikakken albashi ba, saboda yanzu a zaune kawai suke a gida.

Ndume, mamba a jam'iyyar APC, ya bukaci gwamnati ta bawa ma'aikata tallafi idan tana so su zama masu sadaukarwa, da zasu rungumi ragin albashin.

"Ya kamata gwamnati ta yi duba na tsanaki a kan kudaden da take kashewa a kan ma'aikata, wanda ke lashe kusan kaso 70% na kasafin kudi. Akwai bukatar a ingiza kudi domin kaddamar da manyan aiyukan raya kasa.

"Ya kamata mutane su kasance masu sadaukarwa. Wannan lokacine na sake duban al'amura da natsuwa.

Annobar korona: Sanata Ndume ya bukaci FG ta rage albashin ma'aikata
Sanata Ndume
Asali: Facebook

"Sai dai, duk lokacin da na yi magana irin wannan, jama'a su kan fito su sokeni tare da kirana sunaye marasa dadi. Amma hakan ba zai hana na fadi ra'ayina ba.

DUBA WANNAN: Rabon tallafin annobar korona: Matawalle ya caccaki minista Sadiya Farouk

"Akwai bukatar sadaukarwa, musamman a bangaren ma'aikata. Ma'aikata basa zuwa aiki amma ana biyansu cikakken albashi, ana cigaba da kashe musu kudi kamar a lokacin da suke aiki.

"Akwai wani uzuri na cigaba da kashe kudi a kansu? idan mutum ba zai iya aiki a cikin annoba ba, sai a bashi tallafi, a rage masa albashi," a cewar Sanata Ndume.

Gwamnatin tarayya ce ta umarci ma'aikata su zauna a gida domin dakile yaduwar annobar cutar korona.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng