Takarar shugaban kasa a 2023: PDP ta mayarwa da dan Atiku martani

Takarar shugaban kasa a 2023: PDP ta mayarwa da dan Atiku martani

Jam'iyyar PDP ta bayyana cewa tsarin karba - karba ne kadai zai nuna makomar yiwuwar takarar tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar.

An fara maganganu a kasa a kan cewa Atiku zai fito takarar shugaban kasa a zaben shekarar 2023.

Adamu Atiku-Abubakar, ‘dan tsohon mataimakin shugaban kasar Najeriya, Atiku Abubakar, ya ce mahaifinsa zai sake fitowa takarar shugaban kasa a zaben 2023.

Jaridar Punch ta ce Alhaji Adamu Atiku-Abubakar ya bayyana wannan ne a lokacin da ya ke bayani a game da nasarorin da ma’aikatarsa ta samu a jihar Adamawa.

A makon da ya gabata ne Adamu Atiku-Abubakar ya shafe shekaru guda a ofis a matsayin kwamsishinan ayyuka a karkashin gwamnatin PDP ta Ahmadu Finitiri.

Da ya ke bayani a game da nasarorin da ma’aikatarsa ta samu a shekara guda, Adamu Atiku-Abubakar, ya yi magana game da siyasar Najeriya da kuma zaben 2023.

Takarar shugaban kasa a 2023: PDP ta mayarwa da dan Atiku martani
Atiku
Asali: Facebook

Ya ce: “Ni a karon kai na, ban ga wani laifin mahaifina ya fito takarar kujerar shugaban kasa ba. A 2023, mahaifina (Atiku Abubakar) zai yi harin kujera mai darajar farko a kasar nan.”

Da ya ke bada dalilansa, sai ya ce: “Saboda (Atiku) ya kasance kwararren ‘dan siyasa, mai dabara, uban gida, wanda ya kuma lakanci harkar siyasa na kusan shekaru 40.”

DUBA WANNAN: Abin da El-Rufa'i ya fada a kan salon mulkin shugaba Buhari

Atiku ya yi takarar neman kujerar shugaban kasa a inuwar jam'iyyar PDP a zaben 2019, amma sai ya sha kasa a hannun shugaba Muhammadu Buhari, dan takarar jam'iyyar APC.

Da ya ke magana yayin wani taro da manema labarai a Abuja, sakataren yada labaran jam'iyyar PDP, Kola Ologbondiyan, ya ce; "PDP ba ta yanke wata shawara ba a kan tsarin karba - karba. Iya abinda zan iya fada kenan a halin yanzu."

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng