Jerin jihohin Arewa 3 da suka sallami dukkan masu Koronansu

Jerin jihohin Arewa 3 da suka sallami dukkan masu Koronansu

Kimanin watanni uku yanzu da cutar nan mai toshe numfashi da ta addabi duniya watau Coronavorus ko COVID-19 ta bulla a Najeriya.

Alkaluma sun fara nuna an fara samun nasara kan yaki da cutar musamman a Arewacin Najeriya duk da cewa yankin ce kusa ta karce da ta samu bullar cutar a Najeriya.

Kawo yanzu, Najeriya ta samu mutane 11,844 da suka kamu da cutar Coronavirus. Yayinda 3,696 sun samu sauki kuma an sallamesu, 333 sun rigamu gidan gaskiya, a cewar alkaluman hukumar hana yaduwar cututtuka a Najeriya NCDC.

Legit.ng Hausa tana mai kawo muku jerin jihohin Arewa uku da suka alanta sallamar dukkan masu fama da cutar a jihar kuma babu sauran mai cutar a jihohin.

KU KARANTA: Mun sallami karin masu cutar Korona 30 a Abuja - Ministan FCT

1. Jihar Kebbi

A ranar Alhamis, 28 ga Mayu, Kwamitin kar ta kwanan yakar cutar COVID-19 na jihar Kebbi, a ranar Alhamis ya sallami mutum biyu na karshe masu dauke da cutar ta Coronavirus a jihar.

Shugaban kwamitin wanda shine kwamishanan lafiyan jihar, Jafar Muhammad, ya bayyana hakan ne a cibiyar killace masu cutar dake Asibitin KMC dake Kalgo, jihar Kebbi.

Yace: "Mutane biyu masu cutar Coronavirus da suka rage a cibiyar killacewarmu dake asibitin KBC Kalgo sun samu sallama yau, Alhamis, 28/5/2020."

2. Jihar Zamfara

Jihar Zamfara ta sallama majinyata biyar da suka rage mata masu fama da cutar korona a ranar 29 ga watan Mayun 2020.

Kamar yadda hukumar yaki da cututtuka masu yaduwa ta Najeriya (NCDC) ta bayyana, jihar ta fara samun mutane biyu dauke da cutar ne a ranar 24 ga watan Afirilun 2020.

A lokacin kuwa Najeriya na da mutum 1,095 a fadin jihohi 27 wadanda ke dauke da muguwar cutar.

Jimillar adadin wadanda suka kamu da cutar a Zamfara 76. Yayinda 71 suka samu waraka kuma aka sallamesu, 5 sun mutu.

SHIN KA SANYadda zaka rika ganin labaran Legit.ng Hausa a shafinka da dumi-dumi, latsa nan

3. Jihar Sokoto

A ranar Alhamis ne gwamnatin jihar Sokoto ta fitar da sanarwar cewa dukkan ma su dauke da kwayar cutar korona a jihar sun warke sarai.

Hakan na kunshe ne a cikin wani takaitaccen sako da ma'aikatar lafiya ta jihar Sokoto ta wallafa a shafinta da ke manhajar Tuwita.

A cikin sanarwar, gwamnatin jihar ta sanar da cewa an sallami sauran mutane biyar da ke zaman jinyar cutar korona a cibiyar killacewa domin su koma gidajensu, wurin iyalansu.

Mutane 101 ne aka tabbatar da cewa sun kamu da kwayar cutar korona a jihar Sokoto tun bayan bullar cutar, mutane 14 ne cutar ta yi sanadiyar mutuwarsu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng