'Yan bindiga sun kashe mutane 21, sun jikkata 12 a wani sabon hari da ya auku a kauyukan Zamfara

'Yan bindiga sun kashe mutane 21, sun jikkata 12 a wani sabon hari da ya auku a kauyukan Zamfara

Ana zargin wasu gungun 'yan daban daji sun yi wa wasu kauyuka a jihar Zamfara shigar ba zata, inda suka sheke ayarsu wajen zartar da mummunan ta'addanci a kan al'umma.

Mun samu cewa wasu 'yan bindiga sun hallaka mutum 21 tare da jikkata wasu mutane 12, a yayin wani mummunan hari da suka kai wasu kauyuka na jihar Zamfara.

'Yan bindiga sun dugunzuma hankalin al'umma a kauyukan da ke karkashin kananan hukumomin Maru da Talata Mafara a jihar Zamfara kamar yadda Channels TV ta ruwaito.

KARANTA KUMA: Ofishin kasafi: N9b aka ware domin gyara ginin Majalisar Tarayya ba N27b ba

Yayin ganawa da manema labarai, kakakin rundunar 'yan sandan jihar, Muhammadu Shehu, ya ce hare-haren sun auku ne da manufar satar shanu a tsakanin ranar 2 da 3 na watan Yuni.

Shehu ya ce kauyukan da 'yan bindigar suka kai hari a karamar hukumar Maru sun hadar da Tungar Malan, Manyan Karaje, Tungar Arne, Dangodon Maiyakane, Dangodon Mai Masallaci da kuma Boleke.

Sansanin 'Yan daban daji
Hakkin Mallakar Hoto: Channels TV
Sansanin 'Yan daban daji Hakkin Mallakar Hoto: Channels TV
Asali: Twitter

Yana mai cewa, rayuka sun salwanta ne sakamakon fito-na-fito na dakarun 'Yan sa-kai suka yi da maharan, inda aka rika ruwan harsashi na bindiga babu kakkautawa.

Ya ci gaba da cewa, wannan fito-na-fito ta janyo salwantar rayukan mutane 15 yayin da wasu mutum bakwai suka jikkata, wanda a halin yanzu su na ci gaba da samun kulawa a asibiti.

Haka kuma kakakin rundunar 'yan sandan ya bayyana cewa, harin da 'yan bindiga suka kai kauyukan karamar hukumar Talata Mafara, ya salwantar da rayukan mutum 6 yayin da 5 suka jikkata.

DUBA WANNAN: Yadda za ka rika samun labaran Legit.ng Hausa a shafinka ana wallafawa

Kauyukan da aka kai harin a karamar hukumar Talata Mafara sun hadar da Gidan Dan Kani, Tungar lauti, Inwala da kuma Dangodo.

Babban jami'in 'yan sandan ya yi bayanin cewa, 'yan bindiga sun kai munanan hare-haren ne a yayin da al'umma ke dawo wa daga wata sallar Jana'iza.

A halin yanzu bincike ya yi nisa domin bankado miyagun da suka zartar da harin a baya-bayan nan, kuma za su fuskanci hukunci daidai da abinda suka aikata inji Kakakin na 'yan sanda.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng