Dan majalisa Alhaji Tukur Jakada ya rasu bayan gajeriyar jinya

Dan majalisa Alhaji Tukur Jakada ya rasu bayan gajeriyar jinya

Alhaji Tukur Jakada, mamba mai wakiltar mazabar Bakura a majalisar dokokin jihar Zamafara, ya mutu.

Shugaban kwamitin yada labarai na majalisar dokokin jihar Zamfa, Shamsudeen Hassan, ne ya sanar da hakan yayin da ya ke magana da kamfanin dillancin labarai na kasa (NAN) a Gusau, babban birnin jihar Zamfara.

Hassan ya ce Jakada ya mutu ne ranar Lahadi bayan wata gajeriyar jinya.

Kafin mutuwarsa, Jakada ya kasance shugaban kwamitin harkokin kananan hukumomi da sarautu.

'Yan bindiga a jihar Katsina sun kashe shugaban jam'iyyar APC na karamar hukumar Batsari, Abdulhamid Sani Ruma, a kauyensu.

Ruma ya gamu da ajalinsa ne yayin da ya ziyarci kauyensu, Sabon Garin Dunburawa, domin jagorantar rabon gado ga 'ya'yan dan uwansa da 'yan bindiga su ka kashe a shekarar da ta gabata.

Wata majiya ta sanar da Daily Trust cewa wasu 'yan bindiga ne a kan babura, da su ka fito daga jeji, su ka da budewa Ruma wuta, inda ya mutu nan take.

Dan majalisa Alhaji Tukur Jakada ya rasu bayan gajeriyar jinya
Dan majalisa Alhaji Tukur Jakada ya rasu bayan gajeriyar jinya
Asali: UGC

Likitoci sun tabbatar da mutuwarsa bayan an kai gawarsa babban asibitin karamar hukmar Batsari

"Ya bar kauyen nan da misalin karfe 9:00 na safe domin komawa gidansa da ke garin Batsari. Kilomita hudu ne daga kauyen Sabon Garin Dunburawa zuwa garin Batsari.

"Shi kadai aka harbe a cikin mutanen da su ke tare," a cewar majiyar Daily Trust.

DUBA WANNAN: Yadda tsohon gwamnan APC ya dinga biyan kansa alawus din N50m duk bulaguro zuwa Abuja

Mataimakin shugaban jam'iyyar APC na mazabar Katsina ta tsakiya, Mamman Yaro Batsari, ya tabbatar da kisan Ruma.

Ya ce batun kisan Ruma da 'yan bindigar su ka yi, ya jefa jama'a cikin firgici.

"A irin wannan lokacin 'yan bindiga su ka kashe dan uwansa shekarar da ta gabata, yanzu kuma shi ma su ka kashe shi bayan ya ziyarci kauyensu domin rabon gadon dan uwan nasa da aka kashe

"Ya na cikin gonaki yayin rabon gadon ne sai wasu 'yan bindiga su ka bullo daga cikin jeji su ka bude ma sa wuta.

Sabbin hare - haren da 'yan bindiga ke kaiwa a jihohin Katsina da Sokoto a 'yan kwanakin baya bayan nan sun yi sanadiyyar asarar rayukan jama'a da dama tare da raba muttane fiye da 5,000 da gidajensu.

Hare - haren 'yan bindigar sun cigaba da faruwa hatta a cikin wannan lokaci da shugaban kasa, Muhammadu Buhari, ya bawa rundunar tsaro ta kasa umarnin kawo karshen aiyukan 'yan ta'adda a jihohin arewa maso yamma, musamman Katsina da Sokoto.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel