Korona: Mutane 229 sun karu a Najeriya, jimilla ta haura 8,000

Korona: Mutane 229 sun karu a Najeriya, jimilla ta haura 8,000

Hukumar NCDC ta fitar da sanarwar samun sabbin mutane 229 da aka tabbatar da cewa sun kamu da cutar korona a fadin Najeriya a ranar Litinin, 25 ga watan Mayu, 2020.

A cikin sanarwar da NCDC ta saba fitarwa a daren kowacce rana tun bayan bullar annobar korona a Najeriya, jimillar ma su dauke da cutar korona a Najeriya ya haura dubu takwas.

Alkaluman NCDC na ranar Litinin sun nuna jerin jihohi a adadin mutanen da kowacce ta samu daga cikin jimillar ma su dauke da cutar kamar haka;

Lagos-90

Katsina-27

Imo-26

Kano-23

FCT-14

Plateau-12

Ogun-9

Delta-7

Borno-5

Rivers-5

Oyo-4

Gombe-3

Osun-2

Anambra-1

Bayelsa-1

A cewar NCDC, akwai jimillar mutum 8068 da aka tabbatar da cewa su na dauke da kwayar cutar korona a Najeriya, ya zuwa karfe 11:34 na daren ranar Litinin.

An sallami jimillar mutane 2311 daga cibiyoyin killacewa daban-daban da ke fadin kasar nan bayan an tabbatar da cewa sun warke sarai.

Mutane 233 ne suka mutu sakamakon kamuwa da kwayar cutar korona, a cewar alkaluman hukumar NCDC na ranar 25 ga watan Mayu.

DUBA WANNAN: 'Yan N-Power sun tankawa minista Sadiya a kan biyan alawus, sun bukaci ta yi murabus

A wani labarin da Legit.ng ta wallafa, gwamnatin jihar Bauchi ta ce ta na kashe N4,500 domin ciyar da kowanne mai cutar korona da aka kai cibiyar killace ma su cutar a jihar.

Rilwanu Mohammed, shugaban kula da cigaban harkokin lafiya a matakin farko, ne ya sanar da hakan yayin ganawarsa da wakilin kamfanin dillancin labarai na kasa (NAN) a ranar Lahadi.

Ya ce gwamnan jihar Bauchi, Bala Muhammed, ne ya bayar da umarnin a tabbatar cewa ana bawa masu cutar korona isashen abinci a cibiyar.

Wasu daga cikin ma su korona sun yi zanga - zanga domin nuna rashin jin dadinsu a kan yadda aka barsu kara zube a cibiyar killacewa.

Mohammed, shugaban bin diddigin ma su cutar korona a jihar, ya ce gwamna ya bayar da umarnin a tabbatar da cewa ma su cutar sun ji tamkar a gida su ke yayin da su ke cibiyar.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel