Korona: Mutane 229 sun karu a Najeriya, jimilla ta haura 8,000

Korona: Mutane 229 sun karu a Najeriya, jimilla ta haura 8,000

Hukumar NCDC ta fitar da sanarwar samun sabbin mutane 229 da aka tabbatar da cewa sun kamu da cutar korona a fadin Najeriya a ranar Litinin, 25 ga watan Mayu, 2020.

A cikin sanarwar da NCDC ta saba fitarwa a daren kowacce rana tun bayan bullar annobar korona a Najeriya, jimillar ma su dauke da cutar korona a Najeriya ya haura dubu takwas.

Alkaluman NCDC na ranar Litinin sun nuna jerin jihohi a adadin mutanen da kowacce ta samu daga cikin jimillar ma su dauke da cutar kamar haka;

Lagos-90

Katsina-27

Imo-26

Kano-23

FCT-14

Plateau-12

Ogun-9

Delta-7

Borno-5

Rivers-5

Oyo-4

Gombe-3

Osun-2

Anambra-1

Bayelsa-1

A cewar NCDC, akwai jimillar mutum 8068 da aka tabbatar da cewa su na dauke da kwayar cutar korona a Najeriya, ya zuwa karfe 11:34 na daren ranar Litinin.

An sallami jimillar mutane 2311 daga cibiyoyin killacewa daban-daban da ke fadin kasar nan bayan an tabbatar da cewa sun warke sarai.

Mutane 233 ne suka mutu sakamakon kamuwa da kwayar cutar korona, a cewar alkaluman hukumar NCDC na ranar 25 ga watan Mayu.

DUBA WANNAN: 'Yan N-Power sun tankawa minista Sadiya a kan biyan alawus, sun bukaci ta yi murabus

A wani labarin da Legit.ng ta wallafa, gwamnatin jihar Bauchi ta ce ta na kashe N4,500 domin ciyar da kowanne mai cutar korona da aka kai cibiyar killace ma su cutar a jihar.

Rilwanu Mohammed, shugaban kula da cigaban harkokin lafiya a matakin farko, ne ya sanar da hakan yayin ganawarsa da wakilin kamfanin dillancin labarai na kasa (NAN) a ranar Lahadi.

Ya ce gwamnan jihar Bauchi, Bala Muhammed, ne ya bayar da umarnin a tabbatar cewa ana bawa masu cutar korona isashen abinci a cibiyar.

Wasu daga cikin ma su korona sun yi zanga - zanga domin nuna rashin jin dadinsu a kan yadda aka barsu kara zube a cibiyar killacewa.

Mohammed, shugaban bin diddigin ma su cutar korona a jihar, ya ce gwamna ya bayar da umarnin a tabbatar da cewa ma su cutar sun ji tamkar a gida su ke yayin da su ke cibiyar.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng