An kashe 'yan Najeriya 11 a cikin sati uku yayin tabbatar da dokar kulle - NHRC

An kashe 'yan Najeriya 11 a cikin sati uku yayin tabbatar da dokar kulle - NHRC

- Hukumar kare hakin bil'adama ta kasa (NHRC) ta ce jami'an tsaro sun kashe mutane 11 bayan tsawaita dokar hana zirga - zirga

- A rahoto na farko da ta fitar kafin wannan, NHRC ta ce jami'an tsaro sun kashe mutane 18 a cikin sati biyu da saka dokar zaman gida

- A cikin sabon rahoton, NHRC ta ce ta samu korafi 104 na take hakkin bil'adama a cikin sati uku na tsawaita dokar kulle a sassan Najeriya

A kalla mutane 11 aka kashe a sassan Najeriya a cikin sati uku da suka gabata yayin tabbatar da dokar kulle da aka tsawaita saboda dakile yaduwar annobar korona a kasa.

Hakan na kunshe ne a cikin rahoton da hukumar kare hakkin bil'adama ta kasa (NHRC) ta fitar a ranar Litinin.

NHRC ta ce jihar Abia ce a gaba da adada mutane hudu da aka kashe yayin tabbatar da dokar kulle.

A cikin rahoto na farko da ta fitar bayan shafe sati biyu da saka dokar kulle, NHRC ta bayyana cewa jami'an tsaro a Najeriya sun kashe mutane 18 yayin aikin tabbatar da dokar zaman gida, adadin da hukumar ta ce ya zarce na wadanda annobar korona ta kashe.

An kashe 'yan Najeriya 11 a cikin sati uku yayin tabbatar da dokar kulle - NHRC
An kashe 'yan Najeriya 11 a cikin sati uku yayin tabbatar da dokar kulle - NHRC
Asali: Twitter

A cikin sabon rahoton, NHRC ta ce ta samu korafi 104 na take hakkin bil'adama a cikin sati uku na tsawaita dokar kulle a sassan Najeriya.

DUBA WANNAN: Takunkumin fuska ya zama dole a Kano, za a gurfanar da masu kunnen kashi - Ganduje

Babban sakataren NHRC, Barista Tony Ojukwu, ya ce bayan jihar Abia da aka kashe mutane hudu, an kashe mutane biyu a jihar Delta, yayin da aka samu rahoton mutuwar mutum daya a kowacce daga cikin jihohin Neja, Jigawa, Lagos, Anambra da Ribas.

Ojukwu ya ce jami'an rundunar 'yan sanda sun kashe mutane 7 daga cikin mutanen 11, yayin da jami'an hukumar tsaro ta NSCDC da wata hukumar tsaro a jihar Abia suka kashe mutum dai - dai.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel