Yanzu-yanzu: FG ta sakar wa malaman jami'a masu yajin aiki albashi

Yanzu-yanzu: FG ta sakar wa malaman jami'a masu yajin aiki albashi

Malaman jami'o'i da suka tafi yajin aiki a kan sabon tsarin biyan albashi, sun samu albashinsu da gwamnatin tarayya ta rike a yau Juma'a 8 ga watan Mayun 2020.

An gano cewa malaman jami'o'in na bin bashin albashi tun daga na watan Fabariru har zuwa na watan Afirilu, saboda sun ki shiga sabon tsarin gwamnatin tarayya.

A watan Maris ne kungiyar malamai masu koyarwa ta jami'o'i suka bayyana tafiyarsu yajin aiki tun bayan da gwamnatin shugaban kasa Muhammadu Buhari ta hana mambobin ta albashi.

A yayin sassauta hukuncinsa, Shugaba Buhari ya bada umarnin sakin albashin malaman makarantar, jaridar SaharaReporters ta ruwaito.

Amma kuma, har a halin yanzu ba a sani ba ko dukkan malaman sun bi umarni ta hanyar shiga sabon tsarin ko kuma rangwame aka yi musu haka kawai.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng