Jihar Kano ta sha gaban Abuja a yawan ma su dauke da kwayar cutar covid-19

Jihar Kano ta sha gaban Abuja a yawan ma su dauke da kwayar cutar covid-19

A cikin kasa da sati uku da bullar annobar covid-19 a Kano, yanzu haka jihar ta zama ta biyu a yawan ma su dauke da kwayar cutar a Najeriya.

Ana ware adadin mutanen da suka mutu ko aka sallama idan ana duba yawan masu dauke da kwayar cutar covid-19 a jiha ko kasa.

A cikin sanarwar da hukumar yaki da cututtuka ma su yaduwa ta kasa (NCDC) ta fitar ranar Alhamis, jihar Kano ta koma mataki na biyu a yawan ma su dauke da kwayar cutar covid-19 a Najeriya.

Akwai jimillar mutane 136 da aka tabbatar sun kamu da cutar covid-19 a jihar Kano, yayin da jihar Legas, wacce ke mataki na daya, keda jimillar mutane 718 da aka tabbatar kwayar cutar ta harba.

Babban birnin tarayya, Abuja, da a baya ke bin jihar Legas, ya koma mataki na uku da adadin mutane 135 da aka tabbatar suna dauke da kwayar cutar covid-19.

An fara samun labarin bullar annobar covid-19 a Kano a ranar 11 ga watan Afrilu. Wani tsohon jakadan Najeriya ne ya fara kai kwayar cutar Kano daga Abuja.

Masana da kwararru sun bayyana damuwarsu a kan bullar annobar covid-19 a Kano saboda yawan jama'ar da jihar keda su.

Rahotanni na yawan kawo labarin mutuwar mutane a Kano. Amma, gwamnatin jihar Kano ta ce wasu cututtuka daban ne ke kashe mutane, ba annobar covid-19 ba.

Jihar Kano ta sha gaban Abuja a yawan ma su dauke da kwayar cutar covid-19
Cibiyar killace masu cutar covid-19 a Jihar Kano
Asali: Twitter

NCDC ta bayyana cewa ya zuwa yanzu ta gudanar da gwajin kwayar cutar covid-19 a kan mutane 13,689.

Daga cikin jimmilar mutanen da aka gwada, an samu mutum 1,728 da ke dauke da kwayar cutar.

An samu bullar annobar covid-19 a kusan dukkan jihohin Najeriya 36, idan aka cire jihohin Kogi da Kuros Riba, wadanda har yanzu ba a samu rahoton bullar annobar ba.

NCDC ta ce ya zuwa karfe 11:50 na daren ranar Laraba, 29 ga watan Afrilu, akwai jimillar mutane 1728 da aka tabbatar da cewa suna dauke da kwayar cutar covid-19 a Najeriya.

DUBA WANNAN: A karshe, sojojin Najeriya sun kwace kauyen Bula Shatane, 'yan Boko Haram sun mika wuya

An sallami mutane 307 bayan an tabbatar da samun saukinsu, a yayin da cutar ta hallaka jimillar mutane 51.

Alkaluman wadanda annobar covid-19 ta harba da NCDC ke fitarwa a 'yan kwanakin baya bayan nan na nuni da cewa annobar tana kara karfi a arewacin Najeriya.

Kwamishinan lafiya a jihar Borno, Dakta Salihu Kwayabura, ya ce alamu sun nuna cewa kwayar cutar covid-19 ta yadu a tsakanin jama'a. Ya ce akwai bukatar bullo da sabbin dabarun binciko wadanda annobar ta harba.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng