Coronavirus: Jerin jihohi 34 a Najeriya da cutar ta bulla da adadin wadanda suka kamu a kowace jiha

Coronavirus: Jerin jihohi 34 a Najeriya da cutar ta bulla da adadin wadanda suka kamu a kowace jiha

Najeriya na ci gaba da samun hauhawan masu annobar coronavirus, inda a yanzu adadin masu ita ya kai 1,532 kamar yadda alkaluman hukumar yaki da hana yaduwar cututtuka ta Najeriya (NCDC) ta tabbatar.

A daren ranar Talata, 28 ga watan Afrilu, an samu karin mutane 195 da suka kamu, wanda shine mafi yawan adadi da aka samu a kasar cikin rana daya.

A wasu jerin rubutu da ta wallafa a shafinta na Twitter da misalin karfe 11:50 na dare, NCDC ta yi sanarwar yayin da masu coronavirus suka haura dubu daya a cikin kasa da watanni uku bayan an samu bullar cutar a kasar.

80 daga cikin masu cutar sun fito daga Lagas inda Kano ta zama ta biyu a alkaluman da mutane 38 –wadanda shine mafi yawa tun bayan barkewar cutar a jahar.

An salami mutane 255 bayan sun warke daga cutar yayin da 44 suka mutu, sannan har yanzu Lagas ce matattarar cutar a Najeriya.

A duniya gaba daya mutane 3,138,785 ne suka harbu da ccutar a fadin kasashe daban-daban.

KU KARANTA KUMA: PDP ta yi wa El-Rufai wankin babban bargo a kan tsawaita rufe Kaduna na tsawon kwanaki 30

Amma ga rabe-raben masu COVID-19 a kowace jaha, kamar yadda ya ke a alkaluman NCDC yayin da cutar ke yaduwa a fadin jihohin kasar.

1. Lagos: 884

2. FCT: 158

3. Kano: 115

4. Ogun: 50

5. Gombe: 46

6. Osun: 34

7. Katsina: 30

8. Borno: 53

9. Edo: 30

10. Oyo: 21

11. Kaduna: 15

12. Bauchi: 29

13. Akwa Ibom: 12

14.Kwara: 11

15. Sokoto: 19

16. Ekiti: 8

17. Ondo: 8

18. Delta: 7

19 Rivers: 7

20. Taraba: 8

21. Enugu: 3

22. Niger: 2

23. Jigawa: 7

24. Abia: 2

25. Zamfara: 4

26. Benue: 1

27. Anambra: 1

28. Adamawa: 1

29. Plateau: 1

30. Imo: 1

31. Bayelsa: 1

32. Kebbi: 1

33. Ebonyi: 1

34. Nasarawa: 1

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel