Coronavirus: Jerin jihohi 34 a Najeriya da cutar ta bulla da adadin wadanda suka kamu a kowace jiha

Coronavirus: Jerin jihohi 34 a Najeriya da cutar ta bulla da adadin wadanda suka kamu a kowace jiha

Najeriya na ci gaba da samun hauhawan masu annobar coronavirus, inda a yanzu adadin masu ita ya kai 1,532 kamar yadda alkaluman hukumar yaki da hana yaduwar cututtuka ta Najeriya (NCDC) ta tabbatar.

A daren ranar Talata, 28 ga watan Afrilu, an samu karin mutane 195 da suka kamu, wanda shine mafi yawan adadi da aka samu a kasar cikin rana daya.

A wasu jerin rubutu da ta wallafa a shafinta na Twitter da misalin karfe 11:50 na dare, NCDC ta yi sanarwar yayin da masu coronavirus suka haura dubu daya a cikin kasa da watanni uku bayan an samu bullar cutar a kasar.

80 daga cikin masu cutar sun fito daga Lagas inda Kano ta zama ta biyu a alkaluman da mutane 38 –wadanda shine mafi yawa tun bayan barkewar cutar a jahar.

An salami mutane 255 bayan sun warke daga cutar yayin da 44 suka mutu, sannan har yanzu Lagas ce matattarar cutar a Najeriya.

A duniya gaba daya mutane 3,138,785 ne suka harbu da ccutar a fadin kasashe daban-daban.

KU KARANTA KUMA: PDP ta yi wa El-Rufai wankin babban bargo a kan tsawaita rufe Kaduna na tsawon kwanaki 30

Amma ga rabe-raben masu COVID-19 a kowace jaha, kamar yadda ya ke a alkaluman NCDC yayin da cutar ke yaduwa a fadin jihohin kasar.

1. Lagos: 884

2. FCT: 158

3. Kano: 115

4. Ogun: 50

5. Gombe: 46

6. Osun: 34

7. Katsina: 30

8. Borno: 53

9. Edo: 30

10. Oyo: 21

11. Kaduna: 15

12. Bauchi: 29

13. Akwa Ibom: 12

14.Kwara: 11

15. Sokoto: 19

16. Ekiti: 8

17. Ondo: 8

18. Delta: 7

19 Rivers: 7

20. Taraba: 8

21. Enugu: 3

22. Niger: 2

23. Jigawa: 7

24. Abia: 2

25. Zamfara: 4

26. Benue: 1

27. Anambra: 1

28. Adamawa: 1

29. Plateau: 1

30. Imo: 1

31. Bayelsa: 1

32. Kebbi: 1

33. Ebonyi: 1

34. Nasarawa: 1

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng