A yi ma na afuwa: Mun yi kuskure a wajen binne Abba Kyari - PTF

A yi ma na afuwa: Mun yi kuskure a wajen binne Abba Kyari - PTF

Kwamitin fadar shugaban kasa a kan COVID-19, ta bayar da hakuri a kan wasu kura-kurai da aka yi, a lokacin binne marigayi shugaban ma’aikatan shugaban kasa Muhammadu Buhari, Abba Kyari.

An binne Kyari, wanda ya rasu a ranar Juma’a sakamakon annobar coronavirus, a makabartar Gudu da ke Abuja a ranar Asabar.

Yan Najeriya da dama, musamman a shafukan soshiyal midiya, suna ta korafin cewa mafi akasarin wadanda suka halarci jana’izar basu bi umurnin jan tazara a tsakani ba da matakan kariya da ya kamata.

Amma a jawabinsa a ranar Litinin, 21 ga watan Afrilu, Shugaban tawagar na kasa, Sani Aliyu, ya ce kamata ya yi a lura da dandazon jama’ar.

A yi ma na afuwa: Mun yi kuskure a wajen binne Abba Kyari - PTF
A yi ma na afuwa: Mun yi kuskure a wajen binne Abba Kyari - PTF
Asali: Twitter

“Tawagar PTF na bayar da hakuri a kan kurakuran da aka yi a lokacin binne marigayi Shugaban ma’aikatan Shugaban kasa,” in ji PTF din.

“Mun gano cewa ba a daidaita taron jama’ar ba, mun koyi darasi daga wannan kuma za mu tabbatar da hakan bai sake faruwa a gaba ba za a kiyaye tare da bin tsarin kwamitin.

“Tuni aka tsaftace makabartar Gudu, an yiwa kayayyakin kariyar da aka watsar a wajen feshi, sannan aka kona su tare da zubar dasu daidai da tsarin NCDC.

“Zan so yin karin haske kan batun COVID-19 da tsarin binne wanda ya mutu. Sabanin abunda ya ke a soshiyal midiya, an shirya gawar marigayi Shugaban ma’aikatan Shugaban kasa a tsanaki domin binnewa, bisa ga tsarin NCDC da koyarwar addinin Musulunci.

KU KARANTA KUMA: Coronavirus: Gwamna Zulum ya rufe jahar Borno na tsawon kwanaki 14

“Kamar yadda WHO ta bayyana a tsarinta, gawar mutumin da ke dauke da COVID-19 bata harban wani. Har yanzu babu wani hujja da ke nuna cewa mutum zai kamu da cutar don ya hadu da gawar wanda ya mutu sakamakon COVID-19.”

Kwamitin ya ce zai ci gaba da bin tsari da sharudan NCDC wajen binne wanda ke da COVID-19.

Idan ku na da wata shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewa tare da mu.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng