Abba Kyari: Atiku ya yi tsokaci a kan mutuwar shugaban ma’aikatan shugaban kasa

Abba Kyari: Atiku ya yi tsokaci a kan mutuwar shugaban ma’aikatan shugaban kasa

- Atiku Abubakar ya yi tsokaci a kan mutuwar Abba Kyari, shugaban ma’aikatan shugaban kasa Buhari

- Tsohon mataimakin shugaban kasar, ya ce ya kadu da mutuwar Kyari

- Atiku wanda ya kasance dan takarar shugaban kasa na PDP a zaben 2019, ya yi addu’an Allah ya yafe ma Kyari zunubansa sannan ya bashi Aljannah

Tsohon mataimakin shugaban kasar Najeriya, Atiku Abubakar, ya mika ta’aziyyarsa a kan mutuwar Abba Kyari, shugaban ma’aikatan shugaban kasa Muhammadu Buhari.

Fadar shugaban kasa ta sanar da mutuwar Kyari a safiyar ranar Asabar, 18 ga watan Afrilu.

Marigayin ya kamu da cutar COVID-19 sannan kuma yana ta samun kulawar likitoci a wani wuri da ba a bayyana ba.

Abba Kyari: Atiku ya yi martani a kan mutuwar shugaban ma’aikatan shugaban kasa
Abba Kyari: Atiku ya yi martani a kan mutuwar shugaban ma’aikatan shugaban kasa
Asali: UGC

Sai dai kuma, ya rasu a ranar Juma’a, 17 ga watan Afrilu, kamar yadda sanarwa daga kakakin shugaban kasa, Femi Adesina ya nuna.

KU KARANTA KUMA: COVID-19: Fadar shugaban kasa ta bayyana shirye-shiryen jana'izar Abba Kyari

A tsokacinsa, Atiku yace:

"Inna lillahi wa inna ilayhi raji'un. Na yi bakin ciki da mutuwar shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa, Abba Kyari. Allah SWT ya karawa a iyalansa hakuri, Allah ya ji kansa ya yafe masa kura-kuransa, ya saka masa da Aljannah Firdaus. Ameen.”

Labarin yadda ya kamu da cutar ta Coronavirus dai ya fito ne a watan Maris, inda bayan kamuwarshi da cutar, shi ma shugaban kasa Muhammadu Buhari aka yi masa gwaji ba a samu cutar a jikinshi ba.

Shugaba Buhari, Yemi Osinbajo, gwamnoni da ministoci da dama sun hadu da shi kafin a gabatar da gwajin cutar a jikinshi.

Kyari wanda ya dawo Najeriya daga wata tafiya da yayi zuwa kasar Jamus, a ranar 14 ga watan Maris, ya gana da manyan mutane na Najeriya da dama.

Abba Kyari daga baya ya fito ya bayyana cewa za a kai shi birnin Legas daga Abuja domin ya cigaba da karbar magani.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng