Abba Kyari ya fada mani cewa yana nan lafiya – Festus Keyamo

Abba Kyari ya fada mani cewa yana nan lafiya – Festus Keyamo

- Karamin ministan kwadago da daukar ma’aikata, Festus Keyamo, ya yi martani ga mutuwar Abba Kyari, shugaban ma’aikatar Shugaban kasa

- Keyamo ya bayyana a shafin Twitter cewa ya tattauna da Abba Kyari a ranar Talata, 24 ga watan Maris, kafin mutuwarsa

- Ministan ya ce marigayin ya fada masa cewa yana nan lafiya sannan cewa shi (Kyari) zai karbi duk wani magani da za a yi masa

Karamin ministan kwadago da diban ma’aikata, Festus Keyamo, ya kasance dan Najeriya na farko da ya yi martani ga mutuwar Abba Kyari, shugaban ma’aikatan shugaban kasa.

Keyamo ya bayyana a shafin Twitter cewa ya tattauna da Mallam Abba Kyari a ranar Talata, 24 ga watan Maris, kafin mutuwar dan siyasar.

Abba Kyari ya fada mani cewa yana nan lafiya – Festus Keyamo
Abba Kyari ya fada mani cewa yana nan lafiya – Festus Keyamo
Asali: UGC

A cewar ministan, a lokacin tattaunawarsu, marigayi shugaban ma’aikatan tarayyar ya fada masa cewa yana nan lafiya kuma cewa shi (Kyari) zai amshi duk wani magani da za a yi masa cikin aminci.

Keyamo wanda ya mika ta’aziyyarsa ga iyalan Kyari kan mutuwar shugaban ma’aikatan shugaban kasar ya ce, a koda yaushe Allah ya san abunda ya fi dacewa.

“A lokacin da na yi hira dashi a ranar Talata, 24 ga watan Maris, 2020, ya bani tabbacin cewa yana cikin koshin lafiya sannan cewa zai amshi duk wani magani da za a yi masa cikin aminci” in ji ministan.

KU KARANTA KUMA: Yanzu-yanzu: Shugaban ma'aikatan Najeriya Abba Kyari ya riga mu gidan gaskiya

“Amma a koda yaushe Allah ya san abunda ya fi dacewa. Ina mika ta’aziyyata ga iyalan Kyari da gwamnatin Najeriya. Allah ya ji kan Mallam Abba Kyari."

A halin da ake ciki, mun ji cewa za a birne Marigayi Abba Kyari, shugaban ma'aikatan fadar shugaban kasa Muhammadu Buhari a garin Abuja a yau Asabar, jaridar Premium Times ta gano.

Kyari dan asalin jihar Borno ne. An sanar da rasuwarsa ne a jiya Juma’a bayan jinyar da ya kwanta sakamakon kamuwa da yayi da coronavirus.

An gano yana dauke da cutar ne a ranar 23 ga watan Maris kuma an kaishi jihar Legas don jinya.

Bayan rasuwarsa a daren Juma’a, fadar shugaban kasa ta fara shirin birne shi kamar yadda addinin Islama ya tanadar.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng