Jahar Kano ta mika wani mutum da ya kamu da cutar Coronavirus ga gwamnatin Jigawa

Jahar Kano ta mika wani mutum da ya kamu da cutar Coronavirus ga gwamnatin Jigawa

Gwamnatin jahar Jigawa ta sanar da samun mutum na farko dake dauke da annobar cutar Coronavirus, dan asalin jahar Jigawa.

Wani jami’i ya bayyana cewa an turo mutumin jahar Jigawa ne daga jahar Kano, inda a can ne aka gudanar da gwaji a kansa har aka tabbatar da kamuwarsa da cutar.

KU KARANTA: Da dumi dumi: Shugaban kwamitin yaki da Coronavirus a Kano ya kamu da cutar

Premium Times ta ruwaito mutumin matashi ne mai shekaru 26 dan asalin karamar hukumar Kaugamawa, da ya dawo daga jahar Legas.

A kan iyakar jahar Jigawa da Kano jami’in kiwon lafiya na jahar Kano suka kama shi, daga bisani aka gudanar da gwajin cutar Corona akansa, sakamakon gwaji ya tabbatar da hakan.

Kwamishinan ma’aikatar kiwon lafiya ta jahar Jigawa, Abba Zakari ya bayyana cewa a yanzu haka mutumin yana cibiyar killace masu cutar, kuma yana samun lafiya.

Jahar Kano ta mika wani mutum da ya kama da cutar Coronavirus ga gwamnatin Jigawa
Jahar Kano ta mika wani mutum da ya kama da cutar Coronavirus ga gwamnatin Jigawa
Asali: Facebook

“Su biyu ne aka samu yan asalin jahar Jigawa da suka dawo daga jahar Legas, an yi musu gwaji, daya ya kamu, daya kuma bai kamu ba, a yanzu haka suna cibiyar killace masu cutar.” Inji shi.

Kwamishinan ya bayyana wasu matakai da suka dauka a jahar Jigawa don kare yaduwar cutar, inda yace an umarci duk masu zuwa Masallatan Juma’a su yi amfani da abin rufe fuskokinsu.

Haka zalika an nemi Masallatan su tsaya nesa nesa da juna, kimanin mita bibbiyu a tsakani domin kare kansu daga kamuwa da cutar, ko yaduwarta a cikin jama’a.

Gwamnan Jigawa, Muhammad Badaru da kansa ne ya bayyana haka a ranar Alhamis, jim kadan bayan wata ganawa da yayi da sarakunan jahar da sauran masu ruwa da tsaki inda yace:

“Duba da irin abin da yake faruwa a jahar Kano, muna kira ga sarakuna da majalisar malamai su duba tsare tsaren da muka tanadar domin ganin yadda zamu kare jama’anmu ba tare da tsawwala musu ba.

“Shawarar da aka yanke shi ne za mu cigaba da gudanar da sallar Juma’a, amma fa da amincewar za’a bada tazarar mita 2 a dukkanin Masallatai, kuma kowa zai rufe fuskarsa da kyalle ko da ihrami.” Inji shi.

Ku biyo mu a https://facebook.com/legitnghausa

ko a http://twitter.com/legitnghausa

KU LATSA: Hanyar sauko da sabuwar manhajar jaridar Legit.com Hausa cikin sauki

Ga masu shawara ko korafi, a same mu a labaranhausa@corp.legit.com

Sanarwa na musamman: Shafin NAIJ Hausa ya koma Legit Hausa

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng