COVID-19: Gwamnatin Niger ta dage dokar kulle don a yi sallar Juma'a

COVID-19: Gwamnatin Niger ta dage dokar kulle don a yi sallar Juma'a

- Gwamnan jihar Niger, Abubakar Sani Bello ya dage dokar kulle da hana zirga-zirga a jihar don a yi sallar Juma'a

- A makon da ya gabata ne gwamnan jihar Niger din ya saka dokar bayan samun mutum daya da aka yi a jihar dauke da cutar coronavirus

- Kamar yadda aka wallafa a shafin twitter din gwamnan, za a fara sallar Juma'ar ne daga karfe 11 na safe zuwa karfe 3 na yamma sannan dokar ta ci gaba da aiki

Gwamnan jihar Niger, Abubakar Sani Bello, ya dakatar da dokar kulle a jihar don a yi sallar Juma'a.

A makon da ya gabata, gwamnan ya saka dokar kulle ta makonni biyu don hana yaduwar cutar coronavirus a jihar.

Bello ya ce wannan matakin ya zama dole bayan an tabbatar da cewa wani mutum daya na dauke da cutar.

Amma kuma a ranar Juma'a, Lawal Tanko, jami'in yada labarai na sakataren gwamnatin jihar, ya ce za a yi sallar Juma'ar ne a karkashin matakai tsaurara.

DUBA WANNAN: COVID-19: Masari ya dakatar da sallar Tarawihi da Juma'a, ya kuma sake rufe wata karamar hukuma

Tanko ya ce za a yi sallar ne cikin mintuna 30 "za a ci gaba da kullen ana kammala sallar Juma'a".

"Ana amfani da wannan damar don sanar da al'ummar Musulmi a jihar Niger cewa an dage dokar kulle a jihar don yin sallar Juma'a a yau 17 ga watan Afirilun 2020," yace.

Ya kara da cewa, "Za a yi sallar Juma'ar ne a tsakanin karfe 11 na safe zuwa 3 na yamma a karkashin matakai tsaurara. Za a yi amfani da sinadaran kashe kwayoyin cuta, takunkumin fuska da kuma ruwa da sabulu don wanke hannu.

"Dokar nisantar juna za ta yi aiki sannan ba a amince da musabaha ba.

"Ana so a yi huduba da sallar a cikin mintuna 30. Ana shawartar Musulmi da su kiyaye wadannan dokokin don hana yaduwar annobar."

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164