COVID-19: Gwamnatin Niger ta dage dokar kulle don a yi sallar Juma'a

COVID-19: Gwamnatin Niger ta dage dokar kulle don a yi sallar Juma'a

- Gwamnan jihar Niger, Abubakar Sani Bello ya dage dokar kulle da hana zirga-zirga a jihar don a yi sallar Juma'a

- A makon da ya gabata ne gwamnan jihar Niger din ya saka dokar bayan samun mutum daya da aka yi a jihar dauke da cutar coronavirus

- Kamar yadda aka wallafa a shafin twitter din gwamnan, za a fara sallar Juma'ar ne daga karfe 11 na safe zuwa karfe 3 na yamma sannan dokar ta ci gaba da aiki

Gwamnan jihar Niger, Abubakar Sani Bello, ya dakatar da dokar kulle a jihar don a yi sallar Juma'a.

A makon da ya gabata, gwamnan ya saka dokar kulle ta makonni biyu don hana yaduwar cutar coronavirus a jihar.

Bello ya ce wannan matakin ya zama dole bayan an tabbatar da cewa wani mutum daya na dauke da cutar.

Amma kuma a ranar Juma'a, Lawal Tanko, jami'in yada labarai na sakataren gwamnatin jihar, ya ce za a yi sallar Juma'ar ne a karkashin matakai tsaurara.

DUBA WANNAN: COVID-19: Masari ya dakatar da sallar Tarawihi da Juma'a, ya kuma sake rufe wata karamar hukuma

Tanko ya ce za a yi sallar ne cikin mintuna 30 "za a ci gaba da kullen ana kammala sallar Juma'a".

"Ana amfani da wannan damar don sanar da al'ummar Musulmi a jihar Niger cewa an dage dokar kulle a jihar don yin sallar Juma'a a yau 17 ga watan Afirilun 2020," yace.

Ya kara da cewa, "Za a yi sallar Juma'ar ne a tsakanin karfe 11 na safe zuwa 3 na yamma a karkashin matakai tsaurara. Za a yi amfani da sinadaran kashe kwayoyin cuta, takunkumin fuska da kuma ruwa da sabulu don wanke hannu.

"Dokar nisantar juna za ta yi aiki sannan ba a amince da musabaha ba.

"Ana so a yi huduba da sallar a cikin mintuna 30. Ana shawartar Musulmi da su kiyaye wadannan dokokin don hana yaduwar annobar."

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel