An samu karin mutum 35 da suka kamu da coronavirus a Najeriya, jimmila 442

An samu karin mutum 35 da suka kamu da coronavirus a Najeriya, jimmila 442

Hukumar Kula da Cututtuka masu yaduwa ta Najeriya (NCDC) ta tabbatar da samun karin mutum 35 da suka kamu da kwayar cutar COVID-19 wato coronavirus a kasar.

Hakan na nuna cewa jimillar wadanda suka kamu cutar a kasar ya kai 442.

A cewar hukumar ta NCDC sabbin wadanda suka kamu da cutar an samu 19 ne a jihar Legas, 9 a birnin tarayya Abuja, 5 a Kano sai biyu a jihar Oyo.

Hukumar ta bayyana hakan ne a shafin ta na Twitter mai lakabin @NCDCgov kamar yadda ta saba.

A karfe 10:20 na daren ranan Alhamis 16 ga watan Afrilu, an tabbatar da mutane 442 da suka kamu da #COVID19 a Najeriya.

Mutum 152 sun warke an sallame su yayin da mutum 13 sun mutu.

DUBA WANNAN: Shekau ya fadi maganin coronavirus a cikin sabon sakon sautin murya da ya fitar

A wani rahoton, kun ji cewa gwamnan Katsina, Aminu Bello Masari ya sanar da dakatar da yin sallar tarawihi da sallar Juma'a a cikin jami kamar yadda The Cable ta ruwaito.

Gwamnan ya kuma datse shige da fice a karamar hukumar Dutsinma na jihar inda aka samu bullar coronavirus a jihar a ranar Laraba.

Hakan na zuwa ne mako guda bayan Masari ya rufe garin Daura inda mutum na farko da aka samu da cutar a jihar ya rasu.

A cikin sakonni da gwamnan ya wallafa a shafinsa na Twitter a ranar Alhamis, ya bayar da umurnin rufe dukkan manyan kasuwanni a jihar.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164