Hana fita da taron jama'a: An kama babban Limami, an kwace motoci 269 a Abuja

Hana fita da taron jama'a: An kama babban Limami, an kwace motoci 269 a Abuja

Kwamitin tabbatar da biyayya ga umarnin zama a gida da hana taron jama'a a Abuja ya kama wani shugaban al'ummar Musulmi da ya sabawa matakin da hukuma ta dauka domin dakile yaduwar annobar cutar covid-19.

Shugaban kwamitin, Ikharo Attah, ne ya sanar da hakan ga manema labarai a Abuja ranar Lahadi.

Ya kara da cewa, jami'an kwamitinsa sun kwace motoci 269 bayan samunsu da laifin sabawa umarnin a zauna a gida.

"Mun fara aiki da sanyin safiyar yau (Lahadi) bayan wasu 'yan kasa nagari sun kiramu tare da sanar da mu cewa za a yi taron ibada a wata coci da ke unguwar Durumi.

"Bayan mun isa Cocin sai muka iske cewa hakan ba gaskiya bane, amma mun sami Fasto a cikin Cocin tare da masu daukan hoton bidiyo.

"Daga nan sai muka wuce zuwa wani Masallaci da aka tabbatar mana da cewa babban Limamin Masallacin ya jagoranci jama'a sallar Juma'a a yankin Wuye," a cewar Attah.

Ya gargadi jama'a, musamman wadanda ba aikin tsaro suke ba, a kan karya doka.

Hana fita da taron jama'a: An kama babban Limami, an kwace motoci 269 a Abuja
Yayin umarnin hana fita da taron jama'a
Asali: Facebook

A wani labarin mai nasaba da wannan, Legit.ng ta wallafa cewa 'yan sanda a jihar Nasarawa sun kama manyan jami'an gwamnatin jihar da suka karya dokar da gwamnan jihar, Abdullahi Sule, ya kafa a kan killace kai tare da hana taron jama'a saboda dakile yaduwar annobar cutar covid-19.

DUBA WANNAN: Covid-19: Mutane uku sun kara mutuwa a Najeriya, annobar ta shiga jihohi 20

Manyan jami'an gwamnatin da aka kama sune; Alhaji Suleman Agyo, shugaban karamar hukumar Lafiya ta kudu da Mukhtar Wakeel, mukaddashin rijistara a kwalejin kimiyya da fasaha da ke garin Lafiya.

Faifan bidiyon bikin auren shugaban karamar hukumar ya yadu a dandalin sada zumunta, musamman a tsakanin mazauna garin Lafiya.

Da ya ke tabbatar da kama manyan jami'an gwamnatin a ranar Lahadi, kwamishinan 'yan sandan jihar Nasarawa, Bola Longe, ya ce za a gurfanar da su a gaban kotu bisa tuhumarsu da laifin sabawa umarnin gwamnatin jiha.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel