Annobar COVID-19: Fadar Shugaban Najeriya ta lissafo jerin kokarin Buhari

Annobar COVID-19: Fadar Shugaban Najeriya ta lissafo jerin kokarin Buhari

Fadar shugaban kasa ta bakin Femi Adesina ta jero wasu matakai da gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari ta dauko a Najeriya bayan barkewar cutar Coronavirus.

Ga ayyukan da shugaban kasar ya yi daga lokacin da cutar ta fara bayyana zuwa yanzu:

28 ga Junairu: Kafin shigowar cutar Najeriya, gwamnatin tarayya ta tsananta bincike a filayen tashi da saukar jirage a Najeriya da nufin gano masu cutar.

28 ga Junairu: Hukumar NCDC ta bada sanarwar da shirya wadanda za su shawo kan wannan annoba idan har cutar ta barke.

31 ga Junairu: gwamnatin tarayya ta kara shiri a daidai lokacin da WHO ta ce Najeriya ta na cikin wuraren da cutar za ta iya kamari.

27 ga Fubrairu: Ministan lafiyan Najeriya, Dr. Osagie Ehanire, ya sanar da cewa an samu wanda ya fara shigowa da wannan cuta.

9 ga Maris: Buhari ya kaddamar da kwamiti na musamman da zai yi yaki da yaduwar COVID-19.

17 ga Maris: Gwamnatin Najeriya ta dakatar da bikin wasannin da aka shirya za a ayi a Benin, jihar Edo.

18 ga Maris: Shugaban kasa Buhari ya hana wadanda su ka fito daga wasu kasashe 13 shigowa Najeriya.

18 ga Maris: Dakatar da horaswar da ake yi wa masu yi wa kasa hidima a sansanin NYSC a fadin Najeriya.

18 ga Maris: Hukumar NFF da tsaida duk wasu wasannin kwallon kafa na makonni hudu.

18 ga Maris: Diyar shugaban kasa ta killace kanta bayan dawowa daga Ingila.

20 ga Maris: Gwamnatin Najeriya ta rufe Makarantun Sakandare da na gaba da Sakandare.

20 ga Maris: An shigar da wasu kasashen cikin sahun wadanda aka hana shigowa Najeriya.

20 ga Maris: Gwamnati ta rufe filayen sauka da tashin jiragen saman Enugu, Fatakwal da Kano.

21 ga Maris: Hukumar NRC ta dakatar da aikin jiragen kasan Abuja zuwa Kaduna.

KU KARANTA: COVID-19: Buhari zai taimakawa mutum miliyan 11 a Najeriya

Annobar COVID-19: Fadar Shugaban Najeriya ta lissafo jerin kokarin Buhari
Gwamnatin Buhari ta dauki matakan takaita cutar COVID-19 a Najeriya
Asali: UGC

21 ga Maris: Najeriya ta rufe sauran filayen sauka da tashin jiragen Abuja da Legas.

23 ga Maris: CJN, Tanko Muhammad, ya bada umarnin a rufe kotu a Ranar 24 ga Watan Maris.

23 ga Maris: Buhari ya amince da dakatar da taron FEC da NCS a Najeriya.

23 ga Maris: Hukumar zabe na kasa INEC ta tsaida duk wasu aikinta.

24 ga Maris: Hukumar JAMB ta tsaida ayyukanta cak na tsawon makonni biyu.

24 ga Maris: Hukumar NECO ta fasa gudanar da jarrabawar shiga Makarantun Sakandaren gwamnati a fadin Najeriya.

24 ga Maris: Hukumar FCTA ta bada umarnin a rufe shaguna da kasuwanni.

24 ga Maris: Haramta sallah da zuwa coci a birnin tarayya Abuja.

25 ga Maris: An garkame filin sauka da tashin jiragen sama da ke Asaba, Delta.

27 ga Maris: An rufe iyakokin kasan Najeriya.

26 ga Maris: CBN ta bada sanarwar gudumuwar da aka fara badawa domin yaki da cutar COVID-19.

26 ga Maris: Gwamnatin tarayya ta karbi kayan tallafi daga kasar Sin.

27 ga Maris: Gwamnatin tarayya ta ba Legas Naira biliyan 10 domin yaki da annobar COVID-19.

27 ga Maris: Gwamnatin Buhari ta yabawa matakan da CBN ta dauka. An fara shirin sake duba kasafin kudin 2020.

27 ga Maris: Buhari ya bukaci Ma’aikatar kasuwanci da kungiyar MAN su fara hada magunguna da kayan abinci.

27 ga Maris: Ofishin HCSF ya fitar da jawabi, ya na umartar ma’aikata su daina zuwa ofis.

29 ga Maris: Shugaban kasa Buhari ya yi wa ‘Yan kasa jawabi a karon farko.

29 ga Maris: Shugaban kasa ya sa hannu a dokar COVID-19 na shekarar 2020.

30 ga Maris: Dokar hana fita da shugaban kasa ya sa ta fara aiki a Legas da Abuja da kwaye.

Idan ku na da wata shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewa tare da mu.

Asali: Legit.ng

Online view pixel