Yanzu-yanzu: An samu karin mutane 20 sun kamu da cutar Coronavirus, Legas Abuja da Kaduna

Yanzu-yanzu: An samu karin mutane 20 sun kamu da cutar Coronavirus, Legas Abuja da Kaduna

Hukumar takaita yaduwar cututtuka a Najeriya NCDC ta sanar da cewa an samu karuwar mutane ashirin da suka kamu da cutar Coronavirus (#COVID19) a Najeriya.

Hukumar ta bayyana hakan a shafin raayinta na Tuwita ranar Litinin inda tace: “An tabbatar da mutane ashirin sun kamu da #COVID19 a Najerya. 13 a Legas, 2 a Abuja, 2 a Kaduna, .“

“Dai-dai Karfe 9:o0 na daren 30 ga Maris, mutane 131 aka tabbatar sun kamu da COVID19 a Najeriya, an sallami takwas, kuma biyu ya rigamu gidan gaskiya.“

Ga jerin jiha-jiha

Lagos- 81

FCT- 25

Ogun- 3

Enugu- 2

Ekiti- 1

Oyo- 8

Edo- 2

Bauchi- 2

Osun-2

Rivers-1

Benue- 1

Kaduna- 3

Yanzu-yanzu: An samu karin mutane 20 sun kamu da cutar Coronavirus, Legas Abuja da Kaduna
Yanzu-yanzu
Asali: Twitter

Mun kawo muku rahoton cewa Uwargidar Malam Nasir El-Rufai, Hadiza Isma-El-Rufai ta shaidawa Duniya cewa ta ta yi gwajin wannan cuta mai yawo. Amma ba a ji labarin sakamakon ba tukuna.

Hajiya Hadiza Isma-El-Rufai ta yi wannan bayani ne a shafinta na sada zumunta na Tuwita. Mai dakin gwamnan ta kuma godewa addu’o’in da jama’a su ke yi masu.

Hadiza El-Rufai ta nuna cewa Gwawnan ya na ta fama da zaman kadaici na kebewa sauran jama’a, domin gudun yada wannan mummunar cuta ga sauran Bayin Allah.

Isma-El-Rufai ta ce: “Nagode Jama’an Tuwita da duka addu’o’i da fatan alherinku. Mai girma gwamna ya na samun lafiya.”

Har yanzu cutar ba ta fara bayyana a jikinsa ba. Daga baya yau za a yi mani gwaji. Ina sa ran ganin alheri. A halin yanzu mu na cigaba da zaman kebewa jama’a.”

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng