Labari da dumi-dumi: Mutum na biyu ya mutu a Najeriya sakamakon Coronavirus

Labari da dumi-dumi: Mutum na biyu ya mutu a Najeriya sakamakon Coronavirus

Gwamnatin tarayyar Najeriya ta tabbatar da mutuwar mutum na biyu daga cutar coronavirus a kasar.

Ministan lafiya, Dr Osagie Ehanire, ya sanar da hakan a ranar Litinin, 30 ga watan Maris, a lokacin taron tawagar fadar Shugaban kasa kan cutar Covid-19 a Abuja, babbar birnin kasar, Channels TV ta ruwaito.

Ya ce: “Zuwa yanzu, an salami mutum uku bayan sun warke. Amma abun bakin ciki, an kara rasa rai a karshen mako sakamakon mummunan yanayi na rashin lafiya da mara lafiyan ya shiga.

Labari da dumi-dumi: Mutum na biyu ya mutu a Najeriya sakamakon Coronavirus
Labari da dumi-dumi: Mutum na biyu ya mutu a Najeriya sakamakon Coronavirus
Asali: UGC

“Mun jajirce wajen gano wadanda suka yi tarayya kuma manufamu shine hanyar shawo kan lamarin cikin gaggawa, killace su da kuma bibiyar wadanda suka yi tarayya dasu sannan suma a killace su da kuma yi masu magani, domin rage yaduwar cutar.”

“A yau 30 ga watan Maris, 2020, mun samu mutane 111 da aka tabbatar suna dauke da Covid-19 a Najeriya wadanda 68 suka kasance a Lagas, 21 a babbar birnin tarayya, bakwai a Oyo, uku a Ogun, biyu a Bauchi,biyu a Edo, biyu a Osun, biyu a Enugu, sannan daddaya a Benue, Ekiti, da Rivers."

Ya kara da cewa Najeriya ta tabbatar da masu coronavirus 111, cewa mafi akasarinsu wadanda suka dawo daga kasashen waje ne.

A cewar ministan lafiyan, an fi samun yawan wadanda suka kamu a Lagas da Abuja ne saboda sune ,manyan kofofin shigowa kasar.

Ehanire ya gargadi yan Najeriya da su kare tsoffi a cikinsu, da wadanda ke fama da lalura ta rashin lafiya domin sune suke cikin mafi hatsari.

A baya mun ji cewa gwamnatin jihar Legas ta sallam wasu mutane biyar daga cibiyar killacewa da ke asibitin cututtuka masu yaduwa a unguwar Yaba bayan an tabbatar da cewa yanzu basa dauke da kwayar cutar coronavirus.

Ya zuwa yanzu an sallami jimillar mutane 8 kenan daga cibiyar.

Mutanen da aka sallama suna cikin koshin lafiya, babu alamar gajiya ko damuwa a tare da su, kamar yadda jaridar The Nation ta rawaito.

Idan ku na da wata shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewa tare da mu.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng