Yanzu-yanzu: An samu karin masu cutar Coronavirus 4 a yau Lahadi

Yanzu-yanzu: An samu karin masu cutar Coronavirus 4 a yau Lahadi

A yau Lahadi, gwamnatin tarayya ta sanar da cewa na samu karin mutane hudu masu dauke cutar coronavirus (COVID-19), yanzu adadin masu cutar a Najeriya 26.

Hukumar takaita yaduwar cututtuka (NCDC) ta sanar da hakan da safiya Lahadi a shafin raayi da sada zumuntarta na Tuwita.

Jawabin yace “Misalin karfe 08:05 am na ranar 22 ga Maris, an tabbatar da asu dauke da cutar Coronavirus 26 a Najerita. Cikinsu an sallami biyu da suka samu sauki.“

“Don sanin adadin wadanda suka kamu da cutar, ku garzaya http://covid19.ncdc.gov.ng“

Yanzu-yanzu: An samu karin masu cutar Coronavirus 4 a yau Lahadi
Yanzu-yanzu: An samu karin masu cutar Coronavirus 4 a yau Lahadi
Asali: Facebook

A jiya mun kawo muku rahoton cewa A bangare guda, Ministan lafiya, Dakta Osagie Ehanire, ya bayyana cewa an samu karin mutane 10 da suka kamu da cutar Coronavirus a Najeriya.

Ministan ya bayyana hakan ne a shafinsa na Tuwita ranar Asabar, 21 ga watan Maris, 2020.

Yayinda bakwai aka samu a Legas, sauran ukun na birnin tarayya Abuja.

Yanzu dai akwai jimillar masu cutar 22 a Najeriya kuma an sallami biyu da suka samu sauki.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel