Ana zaton wuta a makera: Jami’in hukumar kiwon lafiya ta duniya ya kamu da Coronavirus

Ana zaton wuta a makera: Jami’in hukumar kiwon lafiya ta duniya ya kamu da Coronavirus

Hukumar kiwon lafiya ta duniya, WHO ta bayyana cewa wani babban jami’i dake ofishinta na kasar Iran ya kamu da annobar cutar nan mai suna Coronavirus – Covid-19 da ta addabi al’ummomin duniya gaba daya.

Babban daraktan WHO, Dakta Tedros Ghebreyesus ne ya bayyana haka yayin da yake ganawa da manema labaru inda yace a yanzu haka jami’in da cutar ta kama yana kwance ba shi da lafiya, kamar yadda kamfanin dillancin labaru, NAN, ta ruwaito.

KU KARANTA: Karancin albashi: Gwamnatin Jahar Gombe ba za ta biya kananan hukumomin N30,000 ba

Ana zaton wuta a makera: Jami’in hukumar kiwon lafiya ta duniya ya kamu da Coronavirus
Tedros
Asali: UGC

Tedros yace a yanzu babu inda cutar ta fi kamari kamar Korea, Italy, Iran da kuma Japan, yayin da ake samun saukinta yaduwarta a kasar China, inda ta fara bayyana, don haka Tedros yace a ranar Litinin ma sai da suka kai magunguna da tallafi ga gwamnatin kasar Iran.

“A ranar 1 ga watan Maris an samu rahotanni 206 a kasar China, shi ne mafi karanci a kasar tun daga ranar 22 ga watan Janairu, guda 8 ne kacal daga wajen lardin Hubei, yayin da a wajen China aka samu bullarta sau 8,739 a kasashe 61 tare da mutane 127 da suka mutu a sanadiyyar cutar.” Inji shi.

Sai dai Tedros ya tabbatar da cewa akwai yiwuwar kare yaduwar cutar Coronavirus, wanda yace a yanzu shi ne babban aikin dake gaban kasashen duniya, idan har aka ma cutar tsayuwan daka tabbas kasashen duniya za su dakatar da yaduwar cutar.

A wani labarin kuma, Gwamnatin kasar Saudiyya ta sanar da bullar annobar cutar Coronavirus a kasar, kamar yadda jaridar Saudi Gazette ta bayyana.

Majiyar ta bayyana cewa cutar ta bulla ne a jikin wani dan kasar Saudiyya da ya fito daga kasar Iran, amma ya biyo ta kasar Bahrain, amma zuwa yanzu an killace shi a asibiti, haka zalika an sauki jinin duk mutanen da ya yi mu’amala da su don gudanar da gwaji.

Ku biyo mu a https://facebook.com/legitnghausa

ko a http://twitter.com/legitnghausa

KU LATSA: Hanyar sauko da sabuwar manhajar jaridar Legit.com Hausa cikin sauki

Ga masu shawara ko korafi, a same mu a labaranhausa@corp.legit.com

Sanarwa na musamman: Shafin NAIJ Hausa ya koma Legit Hausa

Asali: Legit.ng

Online view pixel