Wata sabuwa: Mabiya addinin Hindu sun watsawa wani Limamin Masallaci guba a fuska

Wata sabuwa: Mabiya addinin Hindu sun watsawa wani Limamin Masallaci guba a fuska

- Wasu bata-gari ko kuma ‘yan daba mabiya addinin Hindutva sun hari limamin wani Masallaci a kasar India

- Bata-garin sun yi wa limamin masallacin mai shekaru 54 mugun duka ne tare da watsa mishi gubar asid a fuska

- Ba tun yau ba dai aka fara dauki ba dadi tsakanin Musulman kasar Iindia da mabiya sauran addinai a kasar

Wasu ‘yan dabar Hindutva sun hari limamin wani masallaci ta hanyar watsa mishi asid.

Kamar dai yadda aka sani, akwai wata zanga-zanga da Musulman kasar India ke yi sakamakon banbancin da ake nuna musu tun a watan Disamba na 2019.

A jiya ne kuma jaridar Loveforislamic ta walllafa , inda aka tattauna a kan hargitsi da ke aukuwa tsakanin Musulman kasar India da kuma bata-gari.

Wata sabuwa: Mabiya addinin Hindu sun watsawa wani Limamin Masallaci guba a fuska
Wata sabuwa: Mabiya addinin Hindu sun watsawa wani Limamin Masallaci guba a fuska
Asali: Facebook

Wani abu mai tarin ban mamaki ya faru a babban birnin New Delhi a ranar 27 ga watan Fabrairu na 2020. Wani limami ne mai shekaru 54 ne ya sha mugun duka a masallacin Shiv Vihar kafin daga bisani a yayyaga kayan shi tare da watsa mishi asid a fuska.

KU KARANTA: Binciken masana: Nan da shekarar 2050 yawan 'yan Najeriya zai kai miliyan 401

Akwai bukatar duk musulman duniya su taya musulman kasar Indai addu’a a masallatai, salloli da kuma sallolin dare. A kara da neman musu yafiyar Ubangiji a kan zunubbansu.

Babu cikakken bayani game da mutuwar mutane 30 da aka samu a birnin New Delhi din.Da yawa dai an ce wadanda suka rasa rayukan nasu mata ne da kananan yara.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng