Sabbin masarautu: Kotu ta yi watsi da karar masu hannu a nada sabon Sarki

Sabbin masarautu: Kotu ta yi watsi da karar masu hannu a nada sabon Sarki

Mai shari'a Ahmed Tijjani Badamasi na babba kotun jihar Kano yayi watsi da karar masu hannu a nada sarki wacce ke kalubalantar kirkirar sabbin masarautu da kuma zabar sarakunan masu daraja ta farko.

Kamar yadda jaridar Solacebase ta ruwaito, masu hannu a nadin sabon sarkin sun maka Madakin Kano, Hakimin Dawakintofa, Yusuf Nabahani; Makaman Kano, Hakimin Wudil, Abdullahi Sarki-Ibrahim; Sarkin Dawaki Mai Tuta, Hakimin Gabasawa, Bello Abubakar da kuma Sarkin Ban Kano, Hakimin Dambatta, Mukhtar Adnan a gaban kotu.

Sabbin masarautu: Kotu ta yi watsi da karar masu hannu a nada sabon Sarki
Sabbin masarautu: Kotu ta yi watsi da karar masu hannu a nada sabon Sarki
Asali: Instagram

DUBA WANNAN: Dangin amarya sun lakada wa ango duka a wurin liyafar biki

Wadanda ake karar sun hada da gwamnatin jihar Kano, Gwamnan jihar, Kakakin majalisar jihar Kano da kuma kwamishinan shari'ar jihar Kano. Akwai Sarkin Bichi, Alhaji Aminu Ado Bayero; Sarkin Karaye, Alhaji Ibrahim Abubakar; Sarkin Rano, Alhaji Tafida Abubakar da kuma Sarkin Gaya, Alhaji Ibrahim Abdulkadir.

A yayin da aka koma sauraron kara a ranar Litinin, Mai shari'a Ahmed Tijjani Badamosi ya soke hukuncin Mai shari'a Usaman Na'aba wanda ya soke kirkirar sabbin masarautun a ranar 21 ga watan Nuwamba.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel