Sunaye: Zulum ya nada 'yan jihar Anambra da Oyo a gwamnatinsa

Sunaye: Zulum ya nada 'yan jihar Anambra da Oyo a gwamnatinsa

Gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum ya nada Kesta Ogualili daga jihar Anambra da Yusuf Alao daga jihar Oyo a matsayin masu bashi shawara ta musamman.

Ogualili, dan asalin karamar hukumar Dunokofia ne na jihar Anambra yayin da Alao dan asalin karamar hukumar Ogbomosho ta jihar Oyo.

Su biyun na daga cikin mutane 26 da gwamnan ya rantsar a jiya, kamar yadda jaridar The Cable ta ruwaito.

Kamar yadda gwamnan ya sanar, su biyun da ya nada wadanda ba ‘yan asalin jihar Borno din ba ya nada su ne saboda kwarewarsu kuma sun zauna jihar a shekaru aru-aru. Sun kasance masu ruwa da tsaki tare da goyon bayan jam’iyyar APC.

Gwamnan wanda mataimakinsa Umar Kadafur, ya wakilta, ya basu rantsuwar ofishin da aka ba kowannensu.

Sunaye: Zulum ya nada 'yan jihar Anambra da Oyo a gwamnatinsa
Sunaye: Zulum ya nada 'yan jihar Anambra da Oyo a gwamnatinsa
Asali: Twitter

DUBA WANNAN: Dokar zabe: PDP ta kai wa gwamnatin Amurka karar APC

Ga jerin sunayen masu bada shawarar ta musamman gare shi:

1. Modu Mustapha

2. Ali Damasak

3. Mustapha Bulu

4. Hussaini Gambo

5. Bukar Busami

6. Tukur Mshelia

7. Tijjani Modu

8. Inna Galadima

9. Zarah Bukar

10. Mustapha Sandabe

11. Gadau Ngurno

12. Mohammed Maulud

13. Bole Kachallah

14. Abdulrahman Abdulkarim

15. Bashir Maidugu

16. Bukar Konduga

17. Umoru Gaya

18. Ali Zangeri

19. Tukur Ibrahim

20. Tijjani Kukawa

21. Abba Gubio

22. Malam Badu

23. Adamu Chibok

24. Ahmed Zarma

25. Kesta Ogualili

26. Yusuf Alao

Gwamna Zulum ya yi kira ga wadanda aka nada din da su dage don sauke nauyin da aka dora musu.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Tags:
Online view pixel