Sarkin Musulmi da shugaban kiristoci za su tattauna kan mawuyacin halin da ake ciki a Najeriya

Sarkin Musulmi da shugaban kiristoci za su tattauna kan mawuyacin halin da ake ciki a Najeriya

Mai alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Sa’ad Abubakar III tare da shugaban kungiyar kiristocin Najeriya, Samson Olasupo za su gana a wani babban taro da zai gudana a babban birnin tarayya Abuja a ranar Laraba, 22 ga watan Janairu.

Daily Trust ta ruwaito makasudin wannan taro shi ne tattauna halin da Najeriya take ciki. Wannan na daga cikin abubuwan da zasu gudana a yayin taron kungiyoyin addinai na Interfaith Dialogue Forum for Peace (IDFP) karo na 3.

KU KARANTA: Lamari ya ta’azzara: Duk wanda suka zalunce mu Allah Ya tsine musu albarka – Kwankwaso

Shuwagabannin kungiyar, Alhaji Ishaq Kunle Sanni da Bishop Sunday Onuoha ne suka bayyana haka yayin da suke ganawa da manema labaru a Abuja a ranar Talata, 21 ga watan Janairu, inda suka ce akwai dalilin farin ciki a Najeriya, duk da kalubalen da ake fuskanta.

Shuwagabannin biyu sun bayyana cewa akwai cigaba a bangaren tsaro a Najeriya, duk da matsalolin da ake fuskanta. Sa’annan sun tabbatar da bukatar baiwa kowanne dan Najeriya yancin aiwatar da addininsa yadda ya kamata.

A wani labarin kuma, a kokarinsa na rage matsalar cin hanci da rashawa, shugaban hukumar kwastam, Alhaji Hamid Ali ya umarci jami’an hukumar kwastam da su dinga bayyana adadin kadarorinsu a kowanne shekara daga bana.

Ali ya sanar da haka ne a ranar Talata, 21 ga watan Janairu yayin da jami’an hukumar da’ar ma’aikata, CCB, suka kai masa ziyara a ofishinsa a karkashin jagorancin shugaban hukumar, Mohammed Isah.

“Dokar hukumar kwastam ta bukaci duk jami’an kwastam su bayyana kadarorinsu da dukiyoyinsu a duk shekara saboda irin aikin da muke yi, aiki ne na kudi, don haka dole ne mu zama abin koyi ga sauran jama’a.” Inji shi.

Ku biyo mu a https://facebook.com/legitnghausa

ko a http://twitter.com/legitnghausa

KU LATSA: Hanyar sauko da sabuwar manhajar jaridar Legit.com Hausa cikin sauki

Ga masu shawara ko korafi, a same mu a labaranhausa@corp.legit.com

Sanarwa na musamman: Shafin NAIJ Hausa ya koma Legit Hausa

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng