Kau da bara: Limamai sun yi wa Tambuwal addu'o'in samun nasara a kotun koli (Hotuna)

Kau da bara: Limamai sun yi wa Tambuwal addu'o'in samun nasara a kotun koli (Hotuna)

Malaman addinin Islama na jihar Sokoto sun hada sallah ta musamman don neman taimakon Allah a hukuncin da kotun koli zata yanke a kan nasarar Aminu Tambuwal da ake kalubalanta a jihar.

Idan zamu tuna, kotun kolin ta saka ranar 20 ga watan Janairu don jin hukuncin karshe na zaben 9 ga watan Maris na jihohin Kano, Sokoto, Benuwe, Filato da Adamawa.

Jaridar Daily Nigerian ta ruwaito cewa malaman sun hadu ne a babban masallacin idin jihar don yin addu'o'i. Malaman da suka jagoranci addu'o'in sun hada da Malam Tukur Rijiyar-Zaure, Malam Bala Marina, Malam Aliyu Danbaba da sauransu.

Kau da bara: Limamai sun yi wa Tambuwal addu'o'in samun nasara a kotun koli
Kau da bara: Limamai sun yi wa Tambuwal addu'o'in samun nasara a kotun koli
Asali: Facebook

Wasu malaman da suka samu zantawa da manema labarai sun bayyana cewa matukar aka hana jama'ar jihar bukatarsu, suna tsoron zata yuwu zaman lafiya a jihar yayi kaura.

Kamar yadda suka tabbatar, zuwan Tambuwal a matsayin gwamnan jihar ya taimaka wajen fatattakar wasu kalubalen da jihar ke fuskanta wadanda suka hada da luwadi, ta'ammali da miyagun kwayoyi, daba da sauransu.

Kau da bara: Limamai sun yi wa Tambuwal addu'o'in samun nasara a kotun koli
Kau da bara: Limamai sun yi wa Tambuwal addu'o'in samun nasara a kotun koli
Asali: Facebook

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng