Hukuncin kotun koli: Buba Galadima ya yi hasashen abunda ka iya zama makomar Ganduje

Hukuncin kotun koli: Buba Galadima ya yi hasashen abunda ka iya zama makomar Ganduje

Tsohon jigon jam’iyyar Congress for Progressive Change (CPC) kuma tsohon aminin shugaban kasa Muhammadu Buhari, Buba Galadima, a jiya Laraba, 15 ga watan Janairu ya bayyana hukuncin kotun koli wacce ta kaddamar da Hope Uzodinma zababben gwamnan jihar Imo a matsayin babban almara a tarihin duniya.

Ya ce: “Abunda ya faru shine cewa kotun koli a yanzu ta daure kanta saboda ta yaya Za su yiwa Emeka Ihedioha haka sannan su ki yiwa Abba Kabiru Yusuf a Kano? Iri abu guda sak ne ya faru a Kano.

“Idan har ya zama dole a soke zabe, ya kamata ya kasance a matakin rumfar zabe ya kamata a soke a cewar kotun koli. Amma a Kai, ba a soke kuri’un a wajen zabe ba; ba a soke su a matakin unguwa ba sai dai an soke sune a matakin karamar hukuna. Don haka idan har ba a ce Ganduje ya tafi ba sannan aka fadi wani abu sabanin haka, lallai Najeriya za ta ga tashin hankalin.”

Hukumar zabe mai zaman kanta a halin da ake ciki, ta gabatar da takardar shaidar cin zabe ya Uzodinma a jiya Laraba.

KU KARANTA KUMA: Gwamnan Borno ya yi umurnin dakatar da likita kan karkatar da magungunan asibiti

Kwamishinan zabe na kasa da ke kula d Rivers, Bayelsa da Edo, May Agbamuche-Mba be ya gabatar da takardar a lokacin wani kwarya-kwaryan biki da aka shirya a hedkwatar hukumar da ke Abuja.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng