Yan bindiga sun amshe wani gari a Neja, sun fatattaki mutum 2,500

Yan bindiga sun amshe wani gari a Neja, sun fatattaki mutum 2,500

Rahotanni sun kawo cewa an tursasa wa sama da mutane 2,500 a garuruwa daban-daban da ke karamar hukumar Munya na jihar Niger barin gidajensu sakamakon hare-haren yan bindiga.

Lamarin ya kara munana ne da harin ranar Lahadi da yan bindigan suka daukaka, wanda ya yi sanadiyar mutuwar wani babban soja da wasu sojoji uku.

An tattaro cewa yan bindigan sun amshe garin Kabuka sannan sun mayar dashi sansanin aikinsu.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa mutanen da aka fatattaka wadanda mafi akasarinsu mata ne na daukar mafaka a wani makarantar Firamare da ke Sarkin Pawa a hedkwatar karamar hukumar.

Sauran garuruwan da abun ya shafa sune Ingu Kasa, Anguwan Bussa, Galuwi, Almujere, Toko, Anguwan Zarumai da Anguwan Kwata.

Hare-haren ya kuma shafi garuruwan Katarma da Kuduru a karamar hukumar Chikun da ke jihar Kaduna, wacce ke raba iyalan da jihar Niger. Mazauna garuruwan biyu na sun samu mafaka a wasu yankunan jihar Niger.

KU KARANTA KUMA: Sojoji sun mayar wa Gwamna Zulum martani kan zargin da yayi musu

A halin yanzu, gwamnatin jihar Niger ta tura karin jami’an tsaro a garuruwan da abun ya shafa, wadanda tuni sun bi sahun yan bindigan.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Tags:
Online view pixel