Yanzu Yanzu: Yan bindiga sun kai hari Kogi, sun kashe mutum 19 sannan sun kona gidaje da fadar sarki

Yanzu Yanzu: Yan bindiga sun kai hari Kogi, sun kashe mutum 19 sannan sun kona gidaje da fadar sarki

Rahotanni sun kawo cewa yan bindiga sun kashe akalla mutane 19 a garin Tawari a dake karamar hukumar Kogi, jihar Kogi inda suka kona wasu gine-gine ciki harda faar sarkin garin.

Kakakin yan sandan jihar Kogi, Mista Williams Anya, ya tabbatar da faruwar lamarin a wata hira da kamfanin dillancin labaran Najeriya (NAN) a Lokoja a ranar Juma’a, 3 ga watan Janairu.

Ya bayyana cewa tawagar yan sanda sun ziyarci garin sannan cewa an kona gine-gine da dama ciki harda wuraren bauta.

Garin Tawari na yan kilomita kadan da garin Geru a hanyar babban titin Lokoja-Abuja.

Wata mazauniyar Tawari, Misis Comfort Solomon, wacce ta yi nasarar tsira aga harin, ta bayyana cewa yan bindiga kimanin su 100 sun kai mamaya garin a aren ranar Alhamis, 2 ga watan Janairu.

KU KARANTA KUMA: Rundunar sojin sama ta yi kasa-kasa da gine-ginen yan Boko Haram a dajin Sambisa

Ta ce yan binigan sun zo ne a kan Babura sannan suka farma kauyen, ina suka ta kashe-kashe da kone-konen gidaje har zuwa safiyar ranar Juma’a.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng