Wata sabuwa: Za a rushe gine-gine 140 a tsakiyar birnin tarayya

Wata sabuwa: Za a rushe gine-gine 140 a tsakiyar birnin tarayya

- Hukumar da ke kula da tsarin gine-ginen tsakiyar birnin Abuja, ta yi wa gine-gine 140 shaida

- Shugaban bangaren tsari da habaka na yankin, ya ce gine-ginen an yi su ne ba bisa ka'ida ba

- Tuni dai suka sanar da wadanda abun ya shafa tare da basu umarnin tattara komatsansu

Hukumar da ke kula da tsarin gine-ginen tsakiyar birnin Abuja ta yi wa gine-gine 140 shaida don rushewa a yankin Guzape na babban birnin tarayya a Abuja.

A yayin tattaunawa da manema labarai bayan da ya kammala duba gine-ginen, shugaban bangaren tsari da habaka na yankin, Thompson Hope, yace gine-ginen da rusau din ya shafa sune a yankin Kpaduma II da Kuruduma II na Guzape.

DUBA WANNAN: Hukumar Kwastam ta nada sabbin shugabanni, ta yi wa jami'ai 2,408 karin girma (Jerin sunaye)

Ya kara da cewa, gine-ginen da abun ya shafa duk an yi musu shaida kuma an sanar da wadanda ke ciki da su hanzarta tattara komatsansu kafin ranar da za a fara rushe-rushen.

Ya ce, bangaren cigaba da habakar na tarayyar ya dade yana wayar wa da mutanen yankin kai, amma sun ki bin asalin tsarin da wurin ya ginu a kai.

Hope ya ce, ba su kadai ba, akwai wasu wurare na yankin da rusau din zai ritsa dasu kuma duk sunyi shaida. Sun kuma sanar da mutanen yankin.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164

Tags: