Faisal Maina: Dan Abdulrashid Maina da ya zare bindiga a lokacin da za a kama mahaifinsa (Hotuna)

Faisal Maina: Dan Abdulrashid Maina da ya zare bindiga a lokacin da za a kama mahaifinsa (Hotuna)

An gurfanar da Faisal Maina, dan tsohon shugaban hukumar fanshon ma'aikata, Abdulrasheed Maina, a gaban kotu.

A ranar Juma'a ne wata babbar korun tarayya da ke zamanta a Abuja ta bayar da umarnin a tsare Abdulrasheed Maina a gidan yari bayan hukumar EFCC ta gurfanar da shi.

Maina ya gurfana a gaban kotun ne tare da dan sa mai shekaru 20, Faisal, wanda ya zare a lokacin da jami'an tsaro suka yi yunkurin kama mahaifinsa bayan ya shigo Najeriya kimanin sati biyu da suka wuce.

DUBA WANNAN: Rundunar 'yan sanda ta kama dan majalisa a APC daga arewa da hannu dumu-dumu a garkuwa da mutane

Alkalin kotun, Jastis Okon Abang, ya bayar da umarnin tsare Maina ne bisa bukatar hukumar EFCC bayan ya musanta dukkan tuhuma 12 da ake yi masa a gaban kotun.

Alkalin kotun ya daga cigaba da sauraron karar zuwa ranar 30 ga watan Oktoba domin duba takardar bukatar neman beli da Maina ya gabatar ta hannun lauyansa.

Faisal Maina: Dan Abdulrashid Maina da ya zare bindiga a lokacin da za a kama mahaifinsa (Hotuna)
Faisal Maina a Kotu
Asali: Twitter

Faisal Maina: Dan Abdulrashid Maina da ya zare bindiga a lokacin da za a kama mahaifinsa (Hotuna)
Faisal Maina: Dan Abdulrashid Maina da ya zare bindiga a lokacin da za a kama mahaifinsa
Asali: Twitter

Hukumar EFCC ta dade tana farautar Maina domin gurfanar da shi a gaban kotu bisa zarginsa da almundahanar makudan kudaden da ya wawyre lokacin da yake jagorantar hukumar gyaran harkar fansho.

Maina ya sulale ya bar Najeriya a karshen mulkin tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan, bayan an fara bincike a kansa.

Wasu rahotanni sun bayyana cewa an mayar da Maina bakin aiki a gwamnatin shugaba Buhari duk da laifukan da ake zarginsa da aikata wa da kuma kasancewar ya gudu zuwa ketare. Lamarin ya jawo cece-kuce kafin daga bisani maganar ta mutu ba tare da an fahimci gaskiyar zancen ba.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel