Daga karshe Gwamna Masari ya fidda sunayen sabbin kwamishinoninsa kamar haka

Daga karshe Gwamna Masari ya fidda sunayen sabbin kwamishinoninsa kamar haka

Daga karshe bayan daukan dogon lokaci ana shirye shirye, gwamnan jahar Katsina, Aminu Bello Masari ya aika ma majalisar dokokin jahar Katsina jerin sunayen sabbin kwamishinoninsa.

Legit.ng ta ruwaito gwamnan ya mika sunayen mutanen da yake muradin nadawa a majalisar zartarwar gwamnatin jahar Katsina ga majalisar dokokin jahar ne domin tantancesu kamar yadda doka ta shimfida.

KU KARANTA: Ajali ya yi kira: Ruwan kududdufi ya cinye wani mutumi dan shekara 40 a jahar Kano

Wadannan sabbin kwamishinoni sun hada da:

1- Hon Musa Adamu

2- Rt Hon Yau Umar Gwajogwajo

3- Hon Tasiu Dandagoro

4- Hon Abdullahi Imam

5- Hon Dr Rabe Nasir

6- Hon Faruk Jobe

7- Hon Muktar Gidado

8- Hon Sani Aliu Danlami

9- Prof Badamasi Charanchi

10- Hon Abdulkadir Zakkah

11- Tpl Usman Nadada

12- Haj Rabiya Mohd

13- Alh Kasim Umar Mutallab Funtua

14- Alh Abdulkarim Yahaya

15- Hon Mustapha Mahmud Kanti

16- Hon Yakubu Nuhu Danja

17- Hon Hamza Suleman Faskari

Daga karshe majalisar dokokin jahar Katsina ta yanke shawarar fara tantance sabbin kwamishinonin daga ranar Litinin mai zuwa, inda suka zasu tantancesu a rukuni 3, a ranakun Litinin, Talata da Laraba.

Ku biyo mu a https://facebook.com/legitnghausa

ko a http://twitter.com/legitnghausa

KU LATSA: Hanyar sauko da sabuwar manhajar jaridar Legit.com Hausa cikin sauki

Ga masu shawara ko korafi, a same mu a labaranhausa@corp.legit.com

Sanarwa na musamman: Shafin NAIJ Hausa ya koma Legit Hausa

Asali: Legit.ng

Online view pixel