Kwamishinan ‘yan sanda na son a sanya hukuncin kisa ga masu laifukan cin-hanci

Kwamishinan ‘yan sanda na son a sanya hukuncin kisa ga masu laifukan cin-hanci

Alhaji Ali Aji-Janga, Kwamishinan ‘yan sandan jihar Kaduna a ranar Laraba yayi kira ga gwamnatin Najeriya na tayi kwaskwarima ga hukuncin masu laifin cin-hanci ta hanyar sanya daurin rai da rai da kuma kisa a ciki.

Kwamishinan ya fadi wannan maganar ne a yayin da ya halarci wani taro na musamman da aka gudanar a Zaria, inda aka tattauna yadda za iya shawo kan matsalar tsaron Najeriya.

KU KARANTA:Badakkalar naira miliyan 12: EFCC ta kama ma’ajin wata masarauta daga jihar arewa

Kamfanin dillacin Najeriya, NAN ta sanar damu cewa Ali-Janga shi ne babban bako na musamman a wurin taron da kwalejin kimiyya da kere-kere ta Nuhu Bamalli ta shirya.

Kwamishinan wanda ya samu wakilcin ACP Surajo Mohammed-Fana ya ce akwai bukatar an tsaurara hukunci ga masu aikata laifukan cin-hanci ganin yadda yake kawowa Najeriya rashin cigaba.

Ali-Janga ya ce: “Zai yi matukar kyawo idan akayi kwaskwarima ga hukuncin masu laifin cin-hanci da rashawa a Najeriya. Ta hanyar sanya daurin rai da rai da kuma kisan a matsayin hukuncin masu laifin.

“Mutanen da ake samu dumu-dumu da tarin dukiyar jama’a ba kawai karbe kudin za ayi ba, kamata yayi a hanasu sake rike wani mukamin gwamnati gaba daya rayuwarsu.

“Maganar dakile cin-hanci a kasar nan ya kamata a ce ya wuce matakin muhawara a kasar nan yanzu, sai dai a ce wajibine.” Inji Kwamishinan.

Kwamishinan ya kara da yin kira ga matasa a matsayinsu na manyan gobe da suke mike tsaye wurin yaki da cin-hanci a kasar nan, domin gyaran Najeriya.

https://tribuneonlineng.com/cp-advocates-death-penalty-for-corrupt-practices-in-nigeria/

Ku biyo mu a https://facebook.com/legitnghausa

ko a http://twitter.com/legitcomhausa

KU LATSA: Hanyar sauko da sabuwar manhajar jaridar Legit.com Hausa cikin sauki

Ga masu shawara ko korafi, a same mu a labaranhausa@corp.legit.com

Sanarwa na musamman: Shafin NAIJ Hausa ya koma Legit Hausa

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng