Sulaiman Adamu: Ministan Buhari ya ce jiharsa ta fi kowacce jiha kazanta a arewa

Sulaiman Adamu: Ministan Buhari ya ce jiharsa ta fi kowacce jiha kazanta a arewa

Ministan albarkatun ruwa, Suleiman Adamu, ya bayyana cewa gwamnatin jihar Jigawa ta gaza a bangaren tsaftar muhalli biyo bayan kasancewarta mafi koma baya a yankin arewa maso yamma a alkaluman tsaftar muhalli da aka fitar.

Ministan ya bayyana hakan ne ranar Talata, lokacin da ya ziyarci gwamnan jihar Jigawa, Muhammed Badaru Abubakar, a Dutse, babban jihar Jigawa.

Ya ce lamarin bai kamata ya cigaba da tafiya a haka ba tare da yin kira ga gwamna Badaru da ya saka dokar ta baci a bangaren tsaftar muhalli a jihar Jigawa.

Adamu ya jinjina wa gwamnatin jihar Jigawa bisa samun nasara da kaso 86.8 a bangaren samar da ruwan sha mai tsafta ga mutanenta.

"Duk da kasancewar ni dan asalin jihar Jigawa ne, dole mu fada wa kan mu gaskiya cewa jihar Jigawa ta gaza a bangaren tsaftar muhalli. Hakan ne yasa ta zama mafi koma baya a yankin arewa da ma kasa baki daya.

DUBA WANNAN: Wadume: Kwamiti ya bayyana sunan soja da jami'an 'yan sanda 4 da ya kamata a ladabtar

"Duk da jihar Jigawa ta samu nasara da kaso 86.6 a bangaren samar da ruwan sha mai tsafta ga jama'a, amma akwai bukatar inganta tsaftar muhalli," a cewar Adamu.

Da yake mayar da martani ga jawabin Ministan, gwamna Badaru ya amince cewa akwai kalubale ta fuskar tsaftar muhalli a jiharsa tare da bayyana saka dokar ta baci a bangaren kamar yadda ministan ya bukata.

"Za mu ke gudanar da taro kowanne sati domin magance matsalar rashin tsaftar muhalli a jihar Jigawa. Za mu aika kudirin neman haramta yin bahaya a fili zuwa majalisar jihar domin ta yi doka a kai," a cewar gwamna Badaru.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng