Yanzu Yanzu: Sojoji da yan sanda sun mamaye ofishin Sahara Reporters a Lagas

Yanzu Yanzu: Sojoji da yan sanda sun mamaye ofishin Sahara Reporters a Lagas

Rahotanni sun kawo cewa jami’an rundunar yan sandan Najeriya da na sojoji sun yi wa ofishin SaharaReporters, wani jaridar yanar gizo, a jihar Lagas kawanya.

An tattaro cewa ma’aikatan gidan jaridar sun isa wajen aiki da safiyar yau Laraba, 18 ga watan Satumba, amma sai aka hana masu shiga ofishin nasu.

A yanzu haka akwai wata motar yan sanda da aka girke a gaban ofishin. An rahoto cewa jami’an tsaro sun isa harabar wajen da misalin karfe 7:00 na safe sannan suka nemi duk wadanda ke ciki da su fito a nan take.

Hakan na zuwa ne kasa da watanni biyu bayan kama Omoyele Sowore, ma’aikacin jaridar, wanda jami’an yan sandan farin kaya suka kama kan zanga-zangar juyin-juya-hali na kasa baki daya da ya shirya.

An guranar dashi a gaban kotu kan zargin yunkurin kifar da gwamnatin Shugaban kasa Muhammadu Buhari.

KU KARANTA KUMA: Madalla: An kama mutane 3 kan garkuwa da yaran Shugaban karamar hukuma a Katsina

A wani labari na daban, mun ji cewa ‘Dan takarar shugaban kasar jam’iyyar ADC mai adawa a Najeriya a zaben 2019, Obadiah Mailafia, ya bayyana yadda APC ta nemi ya dawo cikin tafiyar jam’iyyar saboda a yafe masa zunubansa.

A Ranar Talata, 17 ga Watan Satumban 2019, Obadiah Mailafia yake cewa jam’iyyar APC mai mulki ta yi kokarin janyo sa a jikin ta da nufin za a yafe masa laifin da bai taba aikatawa a Duniya ba.

A cewarsa, Jiga-jigan APC sun yi tunanin ya na harin shigowa jam’iyyar ne bayan zabe. Mailafia ya yi wannan bayani ne lokacin da ya zanta da Menama labarai a Hedikwatar ADC a Garin Abuja.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng