Shugaba Mnangagwa ya sanar da wurin da za a binne Mugabe

Shugaba Mnangagwa ya sanar da wurin da za a binne Mugabe

Za a binne tsohon Shugaban kasar Zimbabwe, Robert Mugabe a filin binne jarumai na kasa (National Heroes Acre) a watan Oktoba kamar yadda Shugaban kasa Emmerson Mnangagwa ya fadi a ranar Juma'a.

Kafin Shugaban kasar ya yi wannan jawabi, gwamnatin Zimbabwe da iyalan Mista Mugabe ba su cimma matsaya kan wurin da za a binne tsohon shugaban kasar ba.

Da farko an amince cewa za a yi masa jana'iza irin ta muhimman mutane ne a ranar Lahadi a Hiltop Shrine da ke Harare amma mai magana da yawun iyalan Mugabe, Leo Mugabe ya shaidawa manema labarai cewa an soke wannan tsarin.

Za a kai gawar marigayi Mugabe kauyensu na Zvimba a ranar Lahadi domin yi masa wasu addu'o'i na gargajiya kafin daga bisani a binne shi kamar yadda Daily Nigerian ta ruwaito.

DUBA WANNAN: Nasarar Buhari a kotu: Wani dan PDP ya cakawa dan APC kwalba

Za a binne Mugabe a National Heroes Acre a watan Oktoba a cewar Mista Mnangagwa.

An dawo da gawar Mugabe daga kasar Singapore ne a ranar Laraba inda ya rasu yana da shekaru 95 a duniya.

Ya tafi kasar ta Singapore ne inda ya dauki lokaci yana jinyar wata cuta da ba a bayyana ba tun watan Afrilu.

An hambarar da shi daga karagar mulki ne a shekarar 2017 bayan ya shafe kusan shekaru 40 a kan karagar mulki.

Yayin da wasu ke girmama shi saboda gwagwarmayar da ya yi a kan turawan mulkin mallaka, wasu na kyamarsa inda suke ganin shine ya lalata tattalin arzikin Zimbabwe kuma yana yi wa abokan hamayya matsin lamba.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164