Tirkashi: An kori wata ma’aikaciyar banki daga aiki bayan da aka kamata da laifin kwanciya da mazaje 200 masu neman aiki

Tirkashi: An kori wata ma’aikaciyar banki daga aiki bayan da aka kamata da laifin kwanciya da mazaje 200 masu neman aiki

Wata mata dake aikin banki ‘yar asalin kasar Zambia ta rasa aikinta bayan da aka sameta da laifin kanciya da maza 200 wadanda take yiwa alkawarin zata sama masu aiki.

Rahoton da muka samu daga Zambian Watch ya bayyana mana cewa Mutale Winridah ne sunan matar kuma tana rike da babban mukami a bankin ZANACO.

KU KARANTA:Robert Mugabe: Shuwagabannin kasashen Afirka 10 za su halarci jana’izarsa

Matar mai shekaru 39 ta hadu da cikas ne a wurin aikin nata bayan da mutane sama da goma suka kai kararta ga hukumar gudanarwar bankin.

Mutanen dai sun koka kan cewa bayan ta gama amfani da su wurin gamsar da sha’awarta kawai sai tayi watsi da lamarinsu.

Bugu da kari kamfanin dillacin labaran Najeriya NAN ya kawo mana maganar cewa Winfridah dai ba ta da aure kuma ba komi bane ya hana ta yin auren illa son sai ta cinma wani mataki a karatun boko.

https://www.vanguardngr.com/2019/09/breaking-female-banker-sacked-for-sleeping-with-200-male-job-seekers-clients/amp/?__twitter_impression=true

Ku biyo mu a https://facebook.com/legitnghausa

ko a http://twitter.com/legitcomhausa

KU LATSA: Hanyar sauko da sabuwar manhajar jaridar Legit.com Hausa cikin sauki

Ga masu shawara ko korafi, a same mu a labaranhausa@corp.legit.com

Sanarwa na musamman: Shafin NAIJ Hausa ya koma Legit Hausa

Asali: Legit.ng

Online view pixel