Buhari ya sakanka ma jama’an Arewa da manyan mukaman ministoci 14

Buhari ya sakanka ma jama’an Arewa da manyan mukaman ministoci 14

Biyo bayan rantsar da sabbin ministoci da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya yi a ranar Laraba, 21 ga watan Agusta, a iya cewa shugaban kasa ya saurari koken jama’an Arewa, kuma ya share musu hawaye.

Wani bincike da Legit.ng ta gudanar ta hanyar nazari a kan mukaman da shugaban kasa ya baiwa sabbin ministocinsa, yar nune ta nuna shugaba Buhari ya kula da matsalolin yan Arewa, inda ya basu manyan ma’aikatu wadanda suke da matukar muhimmanci ga tattalin arzikin kasa.

KU KARANTA: Hukumar DSS ta bankado wasu mutane 2 dake kokarin kawar da gwamnatin Buhari

Da farko dai shugaban kasa Buhari ya cigaba da rike mukaminsa na babban ministan man fetir, yayin da ya baiwa sabbin ministoci daga jahohin Arewa maso yammacin Najeriya mukamin manyan ministoci ba kanana ba, kamar haka:

1- Suleiman Adamu – Jigawa, ma’aikatan ruwan

2- Zainab Shamsuna Ahmed – Kaduna, ma’aikatan kudi, kasafin kudi da tsare tsare

3- Dr. Mohammad Mahmoud – Kaduna, ma’aikatan muhalli

4- Mohammed Sabo Nanono – Kano, ma’aikatan noma

5- Maj. Gen. Bashir Magashi (rtd) - Kano, ma’aikatan tsaro

6- Hadi Sirika – Katsina, ma’aikatan sufurin jirgin sama

7- Abubakar Malami – Kebbi, ma’aikatan shari’a

8- Mohammed Maigari Dangyadi – Sokoto, ma’aikatan kula da Yansanda

9- Sadiya Umar Faruk – Zamfara, ma’aikatan jin kai, kula da yan hudun hijira da cigaban jama’a

Haka zalika akwai sauran manyan ma’aikata da shugaban kasa Buhari ya aika da jama’an Arewa da suka hada da:

10- Lai Mohammed – Kwara, ma’aikatan watsa labaru

11- Engr. Sale Mamman – Taraba, ma’aikatan lantarki

12- Muhammed Musa Bello – Adamawa, babban birnin tarayya Abuja

13- Adamu Adamu – Bauchi, ma’aikatan ilimi

14) Ali Isa Pantami – Gombe, ma’aikatan sadarwa

Daga karshe akwai wasu kananan ma’aikatu guda 7 da Buhari ya sake nada mutanen Arewa a matsayin kananan ministoci da suka hada da:

1) Abubakar D. Aliyu – Yobe, ma’aikatan ayyyka da gidaje

2) Ramatu Tijani Aliyu – Kogi, ma’aikatan babban birnin tarayya Abuja

3) Gbemisola Saraki – Kwara, ma’aikatan sufuri

4) Amb Maryam Katagum – Bauchi, ma’aikatan kasuwanci da zuba jari

5) Mustapha Baba Shehuri – Borno, ma’aikatan noma

6) Mohammed A. Abdullahi – Nasarawa, ma’aikatan kimiyya da fasaha

7) Amb. Zubairu Dada – Niger, ma’aikatan harkokin waje

A jimlace mutanen Arewa 21 ne suka samu maukamai a cikin sabbin ministocin Buhari

Ku biyo mu a https://facebook.com/legitnghausa

ko a http://twitter.com/legitcomhausa

KU LATSA: Hanyar sauko da sabuwar manhajar jaridar Legit.com Hausa cikin sauki

Ga masu shawara ko korafi, a same mu a labaranhausa@corp.legit.com

Sanarwa na musamman: Shafin NAIJ Hausa ya koma Legit Hausa

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng