An samu rabuwar kai a tsakanin mabiya Zakzaky

An samu rabuwar kai a tsakanin mabiya Zakzaky

Hasashen jama’a sun nuna cewa an samu rabuwar kai a tsakanin mabiya mazhabar Shi’a karkashin jagorancin Sheikh Ibrahim El-Zakzaky.

Hakan ya biyo bayan banbancin ra’ayin da aka samu daga bangarorin mambobin kungiyar ta IMN, akan batun janye zanga-zangar neman a saki shugabansu wanda ke tsare a hannun hukuma tun a shekarar 2015.

A ranar Laraba, 31 ga watan Yuli ne dai mai magana da yawun kungiyar Islamic IMN, Ibrahim Musa ya bayar da sanarwar cewa sun dakatar da zanga-zangar su ta wani lokaci saboda wasu sabbin cigaba da aka samu.

Sai dai kuma a bangare guda Jagoran zanga-zangar, Malam Sunusi Abdulkadir ya ce babu ruwansu da wadanda suka ce wai su sun dakatar da zanga-zanga zuwa wani lokaci inda ya ce su addini su ke yi ba siyasa ba.

Ya kuma jadadda cewa ba za su taba dakatar da zanga-zanga ba har sai lokacin da aka sako Sheikh Zakzaky.

KU KARANTA KUMA: Suhaila Zakzaky ta bayyana cewa yan Shi’a zasu cigaba da zanga zanga a kan tituna

Hakazalilka wata da ke ikirarin cewa 'ya ce ga jagoran mabiya kungiyar mai suna Suhaila Ibrahim Elzakzaky ta bukaci mutanensu da su ci gaba da zanga-zargar da suke yi ta neman a sake jagoran nasu.

Wannan dalilin ne yasa wasu ke ganin cewa wannan karon da suke yi da juna a kan matsayinsu, wata alama ce da ke nuna cewa an samu baraka a tsakanin magoya bayan `yan kungiyar.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng