Shehu Sani ya lissafa muhimman dalilai 5 da ke janyo rashin tsaro a Najeriya

Shehu Sani ya lissafa muhimman dalilai 5 da ke janyo rashin tsaro a Najeriya

- Shehu Sani ya yi tsokaci kan kallubalen rashin tsaro da ake fama da shi a kasar inda ya lisaffa dalilai biyar

- Ya ce dalilai biyar din ne manyan abubuwan da ke haifar da rashin tsaro a Najeriya

- Sanatan ya ce rashin tattaunawa tsakanin mutane da rashin yaki da rashawa suna daga cikin dalilan

Sanata Shehu Sani ya lissafa dalilai biyar da ke asassa rashin tsaro a Najeriya duk da cewa an kwashe kimanin shekaru goma ana kokarin magance matsalar.

Kamar yadda ya lissafa a shafinsa na Twitter a ranar Juma'a 19 ga watan Yuli, Sani ya ce yaki da ta'addanci, sayar da makamai a duniya suna daga cikin dalilan.

DUBA WANNAN: Da dumi-dumi: Atiku da PDP sun kammala gabatarwa kotu shaidunsu 62

Ga cikaken dalilai biyar da sanatan ya bayar:

1 - Rashawa wurin yaki da rashawa

2 - Rashin tattaunawa tsakanin al'umma

3 - Jefa siyasa cikin harkar tsaro

4 - Yadda ake jifa siyasa wurin sayarwa Najeriya makamai

5 - Tallafin da kungiyoyin ta'addan Najeriya ke samu daga kasashen ketare

Idan ba a manta ba Legit.ng ta ruwaito cewa 'yan kungiyar Boko Haram sun yi wa wata mota dauke da ma'aikatan Action Against Hunger kwantar bauna a hanyarsu ta zuwa Damasak a jihar Borno.

Shashwat Saraf, shugaban kungiyar a Najeriya ya ce harin ya afku ne a ranar Alhamis 18 ga watan July.

Ya ce: "A ranar Alhamis 18 ga watan Yuli sun kaiwa tawagar motoccin mu hari a Damasak a jihar Borno a Najeriya. An kashe direban guda daya, yayin da ma'aikatan kungiyar da sauran direbobin biyu da ma'aikatan lafiya uku kuma ba a gansu ba."

Saraf ya bayyana damuwarsu kan afkuwar harin inda ya ce za suyi kokarin gano mutanen da suka bace domin sada su da iyalansu.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164

Tags: