Yadda wani dattijo mai shekaru 73 ya angonce da amarya mai shekaru 63 a Zaria

Yadda wani dattijo mai shekaru 73 ya angonce da amarya mai shekaru 63 a Zaria

Wani bikin aure tsakanin wasu dattijai biyu; namiji mai shekaru 73 da wata mata mai shekaru 63, ya jawo cece-kuce a tsakanin 'yan Najeriya ma'abota amfani da dandalin sada zumunta.

A cewar Chinecherem Ebubechi, mutumin da ya fara yada hotunan bikin dattijan a dandalin sada zumunt, ya ce angon, Matthew Owojaiye, mai shekaru 73, ya auri sahibarsa, Abosede Ayobola, mai shekaru 63.

A cewar Chinecherem, ango Matthew, malamin addinin Kirista, ya auri Ayobola ne a karo na farko tun farkon fara soyayyarsu, shekaru 50 da suka wuce.

Ya bayyana cewa bayan haduwarsu ta farko a wancan lokacin, Mathew ya gayyaci Ayobola domin su fita tare amma sai ta ki amincewa da hakan.

Soyayyarsu ta kullu ne bayan sun sake haduwa a karo na biyu bayan wasu shekaru masu yawa. Duk tsawon wannan lokacin babu wanda ya yi aure a tsakaninsu, hakan ne ma ya sa suka yanke shawarar bawa juna dama har so ya kullu a tsakaninsu.

Sun yi aure a Cocin 'Living Faith' da ke garin Zaria a gaban 'yan uwa da abokan arziki'

Yadda wani dattijo mai shekaru 73 ya angonce da amarya mai shekaru 63 a Zaria
Amarya da Ango da abokan arziki
Asali: Twitter

Yadda wani dattijo mai shekaru 73 ya angonce da amarya mai shekaru 63 a Zaria
Dattijo mai shekaru 73 ya angonce da amarya mai shekaru 63 a Zaria
Asali: Twitter

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng