Yadda wayar salula ta yi sanadiyyar mutuwar wani saurayi

Yadda wayar salula ta yi sanadiyyar mutuwar wani saurayi

- Wayar salula ta yi sanadiyyar mutuwar wani saurayi a kasar Thailand

- An iske gawar saurayin ne a kwance a kan gado yayin da wayar tashi take caji a kusa dashi

Wani mutumi dan shekaru 22 a duniya daga kasar Thailand ya rasa ransa sanadiyyar wayar salula da ya sanya caji a kan gadon ya kuma kwanta bacci.

A cewar jaridar Dailymail, mutumin wanda ba a bayyana sunansa ba yana zaune shi daya ne a cikin dakin nashi inda yake jiran sauran 'yan uwanshi su karaso garin da yake mai suna Nakhon Ratchasima ranar Litinin da dare. A lokacin da 'yan uwan nashi suka zo dakin nashi, sun iske gawar shi ga kuma wayar tashi nan kusa dashi tana makale a jikin abin cajin.

Yadda wayar salula ta yi sanadiyyar mutuwar wani saurayi
Yadda wayar salula ta yi sanadiyyar mutuwar wani saurayi
Asali: Facebook

Mutuwar mutumin ta zo watanni kadan bayan wani ma'aikacin kamfani shima wayar tayi sanadiyyar kashe shi a lokacin da ya sanya ta caji kuma yake amfani da abin jin kida na kunne a lokaci daya a kasar Thailand din. An samu gawar Kritsada Supol a kan gadonsa da wayarsa jone a jikin wuta a watan Fabrairun wannan shekarar.

KU KARANTA: Wata mata ta bayyana yadda ta yi mutuwar karya yayin da 'yan bindiga suka kashe duka danginta a jihar Filato

Mai gidan da yake haya yaje dakin marigayin da safiyar ranar da lamarin ya faru inda ya iske gawar shi kwance akan gado da alamar konewa a kunnensa. Haka ya nuna cewa yana jin kida ne ko kuma waya da wani lokacin da lamarin ya faru.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Latsa nan: Domin karuwa cikin wannan wata mai alfarma na Ramadana

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng