Kai tsaye: Bikin rantsar da shugaban kasa da mataimakinsa
An rufe taron rantsar da Shugaba Buhari da Mataimakinsa Osinbajo. Sai dai shugaban bai yi jawabi ba, kamar yadda ya yi a shekarar 2015 lokacin da ya dauki rantsuwar fara mulkin wa'adinsa na farko.
An karanto tarihin Shugaba Buhari yayin da shi kuma yake ci gaba da kewaye dandalin Eagle Square a cikin wata mota yana jinjina ga jama'a.
Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya dauki rantsuwar kama aiki a matsayin shugaban kasar Najeriya a karo na biyu a yau Laraba, 29 ga watan Mayu.
Shugaban alkalan Najeriya, Justis Mohammed Tanko ne ya rantsar da shugabannin biyu.
A yanzu haka, mataimakin shugaban kasa, Farfesa Yemi Oinbajo ya dauki rantswar kama aiki a karo na biyu.
Farfesa Shehu Galadanci ne zai bude taron rantsa da shugabannin da addu'ar addinin Musulunci.
Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya isa dandalin Eagle Square da ke Abuja, inda za a rantsar da shi tare da Mataimakinsa Yemi Osinbajo a wa'adin mulki na biyu.
Mataimakin shugaban kasa, Osinbajo ma ya isa dakin taro na Eagle Sqare.
Tsohon Shugaban kasa a mulkin soja, Janar Yakubu Gowon da tsohon Shugaban kasa, Cif Ernest Shonekan na daga cikin manyan mutanen da suka isa filin taro na Eagle Square a Abuja, wajen bikin rantsar da Shugaban kasa a yau Laraba, 29 ga watan Mayu.
Za a rantsar da Shugaban kasa Muhammadu Buhari da mataimakin Shugaban kasa, Yemi Osinbajo a wajen taron.
Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa har yanzu tsoffin Shugabannin kasa Olusegun Obasanjo da Ibrahim Badamasi Babangida basu hallara ba a wajen taron.
Sauran manyan mutanen da suka hallara sun hada da mambomin kungiyar sojojin diflomasiyya, manyan yan kasuwa, Aliko Dangote, gwamnoni, jiga-jigan jam’iyyar All Progressives Congress (APC), yan majalisa da sauransu.
An tattaro cewa an tsaurara matakan tsaro a wajen taron.
KU KARANTA KUMA: Gwamnatin tarayya za ta samar da ayyuka miliyan 20 a zangon Buhari na 2 - Minista
A baya Legit.ng ta rahoto cewa ma’aikatan FRSC akalla 2000 za a jibge a cikin babban birnin tarayya Abuja a dalilin bikin rantsuwar da ake yi yau Laraba 29 ga Watan Mayu.
Wani babban jami’in hukumar FRSC masu kula da tituna a Najeriya, Mista Gora Wobin, ya bayyana cewa za a baza ma’aikata da za su lura hanyoyi a yayin da ake sake rantsar da shugabannin Najeriya.
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewa tare da mu.
Ga masu bukatar manhajar mu na Azumi a wannan wata mai albarka sai a bibiyi wannan shafi https://fb.gg/play/ramadan_ramadan
Asali: Legit.ng