Kai tsaye: Bikin rantsar da shugaban kasa da mataimakinsa

Kai tsaye: Bikin rantsar da shugaban kasa da mataimakinsa

An rufe taron rantsar da Shugaba Buhari da Mataimakinsa Osinbajo. Sai dai shugaban bai yi jawabi ba, kamar yadda ya yi a shekarar 2015 lokacin da ya dauki rantsuwar fara mulkin wa'adinsa na farko.

An karanto tarihin Shugaba Buhari yayin da shi kuma yake ci gaba da kewaye dandalin Eagle Square a cikin wata mota yana jinjina ga jama'a.

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya dauki rantsuwar kama aiki a matsayin shugaban kasar Najeriya a karo na biyu a yau Laraba, 29 ga watan Mayu.

Shugaban alkalan Najeriya, Justis Mohammed Tanko ne ya rantsar da shugabannin biyu.

Kai tsaye: Bikin rantsar da shugaban kasa da mataimakinsa
Kai tsaye: Bikin rantsar da shugaban kasa da mataimakinsa
Asali: Twitter

A yanzu haka, mataimakin shugaban kasa, Farfesa Yemi Oinbajo ya dauki rantswar kama aiki a karo na biyu.

Kai tsaye: Bikin rantsar da shugaban kasa da mataimakinsa
Mataimakin shugaban kasa Yemi Osinbajo a lokaccin da ake rantsar da shi
Asali: UGC

Farfesa Shehu Galadanci ne zai bude taron rantsa da shugabannin da addu'ar addinin Musulunci.

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya isa dandalin Eagle Square da ke Abuja, inda za a rantsar da shi tare da Mataimakinsa Yemi Osinbajo a wa'adin mulki na biyu.

Mataimakin shugaban kasa, Osinbajo ma ya isa dakin taro na Eagle Sqare.

Tsohon Shugaban kasa a mulkin soja, Janar Yakubu Gowon da tsohon Shugaban kasa, Cif Ernest Shonekan na daga cikin manyan mutanen da suka isa filin taro na Eagle Square a Abuja, wajen bikin rantsar da Shugaban kasa a yau Laraba, 29 ga watan Mayu.

Za a rantsar da Shugaban kasa Muhammadu Buhari da mataimakin Shugaban kasa, Yemi Osinbajo a wajen taron.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa har yanzu tsoffin Shugabannin kasa Olusegun Obasanjo da Ibrahim Badamasi Babangida basu hallara ba a wajen taron.

Sauran manyan mutanen da suka hallara sun hada da mambomin kungiyar sojojin diflomasiyya, manyan yan kasuwa, Aliko Dangote, gwamnoni, jiga-jigan jam’iyyar All Progressives Congress (APC), yan majalisa da sauransu.

An tattaro cewa an tsaurara matakan tsaro a wajen taron.

KU KARANTA KUMA: Gwamnatin tarayya za ta samar da ayyuka miliyan 20 a zangon Buhari na 2 - Minista

A baya Legit.ng ta rahoto cewa ma’aikatan FRSC akalla 2000 za a jibge a cikin babban birnin tarayya Abuja a dalilin bikin rantsuwar da ake yi yau Laraba 29 ga Watan Mayu.

Wani babban jami’in hukumar FRSC masu kula da tituna a Najeriya, Mista Gora Wobin, ya bayyana cewa za a baza ma’aikata da za su lura hanyoyi a yayin da ake sake rantsar da shugabannin Najeriya.

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewa tare da mu.

Ga masu bukatar manhajar mu na Azumi a wannan wata mai albarka sai a bibiyi wannan shafi https://fb.gg/play/ramadan_ramadan

Asali: Legit.ng

Online view pixel