An kashe mutum 50, an raunta 30 bayan an kai hare-hare a Zamfara

An kashe mutum 50, an raunta 30 bayan an kai hare-hare a Zamfara

‘Yan bindiga sun hallaka Bayin Alla da-dama a wasu hare-hare har 3 da aka kai a cikin Garuruwan jihar Zamfara a karshen makon jiya. Jaridar Punch ta rahoto adadin mutanen da aka kashe a jihar.

Akalla mutane 50 ne aka hallaka, bayan an ji wa wasu 31 rauni a cikin hare-haren da aka kai cikin Zamfara kwanan nan. Wasu ‘Yan bindiga dai sun hana mutanen yankin Dangurgu, kunkilai, da Birnin Magaji sakat a cikin kwanakin nan.

Hari 3 aka kai a cikin wadannan Garuruwa da ke cikin kananan hukumomin Maru, Gusau da kuma Birnin Magaji a karshen makon da ya gabata, Hakan na zuwa ne bayan jami’an tsaro sun yi azamar kawo karshen ta’adin da ake yi a jihar.

KU KARANTA: Abin da ya sa aka gaza kawo karshen matsalar satar mutane

An kashe mutum 50, an raunta 30 bayan an kai hare-hare a Zamfara
Mutune 50 su ka sheka barzahu a sabon kashe-kashen Zamfara
Asali: Twitter

Dakarun ‘yan sanda sun kaddamar da wani shiri na ‘Operation Puff Adder’ da ake sa rai zai kawo karshen kashe mutanen da ake yi a Garuruwan Zamfara da kewaye. Amma sai ga shi an kashe mutum 50 a Ranar Asabar da ta wuce.

Kamar yadda mu ka samu labari, wadannan ‘yan bindiga sun shiga Kauyen Kunkilai ne a Ranar 4 ga Watan Mayun nan inda su ka budawa wasu masu halartar bikin suna wuta. A nan-take aka kashe mutane 30, kuma aka raunata mutum 6.

A Ranar Juma’a kuma ‘Yan bindiga su ka kashe mutum 20 a Garin Magami da ke cikin Gusau, an kuma yi wa mutum 15 rauni a harin daga ciki har da sojoji. Jami’an tsaro sun tabbatar da aukuwar wannan hari bayan ‘yan bindigan sun tsere.

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewa tare da mu.

Asali: Legit.ng

Online view pixel