'Yan Shi'a sun kutsa kai cikin dakin majalisar wakilai a Abuja

'Yan Shi'a sun kutsa kai cikin dakin majalisar wakilai a Abuja

- An tilastawa 'yan majalisar wakilai na tarayya daga taron su, bayan 'yan shi'a masu zanga-zanga da ke Abuja sun kutsa kai cikin dakin taron majalisar da ke Abuja

- 'Yan shi'an wadanda suka shafe shekaru suna zanga-zanga da nuna bukatar gwamnati ta saki jagoransu, bayan kama shi da ta yi a watan Disambar shekarar 2015

A jiya Laraba ne 24 ga watan Afrilu, majalisar wakilai ta tarayya dakatar da zaman da ta ke yi babu shiri, jim kadan bayan 'yan shi'a masu zanga-zanga sun kutsa kai cikin dakin majalisar ta karfin tsiya.

Mataimakin kakakin majalisar wakilai na kasa, Yusuf Lasun, ya ce 'yan shi'ar wadanda suke gabatar da zanga-zanga sun karya kofar shiga majalisar ta farko suka kutsa kai cikin dakin majalisar. Hakanne ya tilasta majalisar dakatar da zaman da ta ke yi.

'Yan Shi'a sun kutsa kai cikin dakin majalisar wakilai a Abuja
'Yan Shi'a sun kutsa kai cikin dakin majalisar wakilai a Abuja
Asali: Facebook

'Yan Shi'an sun gudanar da zanga-zanga babu adadi a fadin kasar nan, suna bukatar gwamnati ta saki jagoransu, wanda ta kama tun watan Disambar shekarar 2015.

An kama shugaban na su, Ibrahim El-Zakzaky, tare da matarsa Zeenaat, bayan sojoji sun kashe daruruwan 'yan shi'ar a Zaria, jihar Kaduna, a tsakanin 12 ga watan Disamba zuwa 15 ga watan Disambar shekarar 2015. Wasu daga cikin 'ya'yan El-Zakzaky suma sun mutu sakamakon zuwan sojojin.

KU KARANTA: Ya kashe 'yan uwar budurwarshi su takwas saboda ta ce ba ta son shi

Akalla mutane 347 ne aka tabbatar da mutuwarsu kuma an binne su a Kaduna.

Har ya zuwa yanzu El-Zakzaky da matarsa Zeena, na nan a tsare, bisa zargin da ake yi musu na kashe soja.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel